Zamu Kama Duk Wani Matafiyi mai dauke da Gwajin COVID19 na Bogi, NCDC

Zamu Kama Duk Wani Matafiyi mai dauke da Gwajin COVID19 na Bogi, NCDC

- Hukumar NCDC ta baygana cewa zata cafke duk wani matafiyi da ta kama ɗauke da sakamakon gwajin cutar korona na bogi

- Shugaban Hukumar Chikwe Ihekweazu ya bayyana haka a taron kwamitin yaƙi da cutar korona a Abuja.

- Yace sun gano wani ɗakin gwaje-gwaje da ke ɗaukar nauyin bada wannan sakamakon kuma sun rufe shi

Hukumar kiyaye yaɗuwar cututtuka ta ƙasa (NCDC) ta ce duk wani matafiyi da aka samu da sakamakon gwajin korona na bogi za'a kama shi kuma zai fuskanci hukunci.

Shugaban hukumar NCDC, Chikwe Ihekweazu, ya bayyana haka ya yin da yake jawabi a taron kwamitin yaƙi da cutar COVID19 ranar Litinin.

KARANTA ANAN: Yan bindigan da suka sace Sarkin Gargajiya A Jihar Ogun sun Buƙaci a basu 100 Miliyan

Shugaban ya ce an ƙaddamar da shafi na musamman don tabbatar sakamakon gwajin.

Jaridar The Cable ta ruwaito cewa, wasu matafiya na biyan jami'an gwamnati kuɗi don su basu sakamakon gwajin na ƙarya.

Bayan wannan rahoto ne, gwamnatin tarayya ta binciko ɗakin gwajin dake wannan aikin kuma ta rufe shi.

Ihekweazu ya ƙara jaddada cewa duk wani matafiyi da yazo da gwajin ƙarya filin sauka da tashin jiragen sama za'a cafke shi kuma za'a hukunta shi.

Haka zalika, shugaban ya ce daga yanzu duk wani gwaji da aka yi a ɗakin gwaji mai zaman kanshi sai jami'an lafiya na filin jirgi sun bincike shi.

Zamu Kama Duk Wani Matafiyi Dake Da Gwajin COVID19 Na Bogi, NCDC
Zamu Kama Duk Wani Matafiyi Dake Da Gwajin COVID19 Na Bogi, NCDC Hoto: @NCDCgov
Asali: Twitter

"Da yawa daga cikin ku kunji maganar da nayi a baya kan shafin tantance sakamakon gwajin korona, to wannan shafin ya fara aiki yanzu," Ihekweazu ya faɗa.

"A satin da ya gabata, mun miƙa matafiya da yawa ga hukumonin tsaro saboda kama su da sakamon gwajin bogi da muka yi."

KARANTA ANAN: Kamfanin MTN ya bai wa Najeriya gudunmawar alluran Korona guda 300,000

"Wani lokacin jami'an mu ne ke bada wannan sakamakon na ƙarya, amma daga yanzin duk wanda muka kama to ya kuka da kansa."

Ya ƙara da cewa: "Muna ba yan Najeriga shawara, duk wanda zai yi tafiya zuwa wata ƙasa to ya tabbatar ya yi gwajin COVID19 a wuraren da aka amince da su wanda za'a iya gani a shafin mu na yanar gizo."

"Kafin ka yi tafiya, ka duba ƙasar da zaka idan suna da buƙatar sakamakon dole, to ka garzaya ka yi a wuraren da aka amince da su, domin zaka samu sakamakon da aka amince da shi a ko ina. Hakan yana da matukar amfani."

A wani labarin kuma EFCC za ta binciki 'yan Najeriya da ke rayuwar da ta fi karfinsu a shafukan sada zumunta

Mataimakiya ga shugaban kasar Najeriya kan kafofin sada zumunta, Laurette Onochie, ta ce hukumomin da ke yakar cin hanci da rashawa wato EFCC da ICPC za su binciki 'yan Najeriya da ke rayuwar da ta fi ƙarfinsu musamman a shafukan sada zumunta.

Wannan ya biyo bayan umarnin da shugaban EFCC ya bayar na bincikar ma'aikatan banki.

Ahmad Yusuf sabon ma'aikacin legit.ng ne ɓangaren Hausa, ya fara aiki kwa nan nan. Yana kawo rahotanni a ɓangare daban-daban.

Ya yi karatun digirinsa na farko a Jami'ar kimiyya da fasaha dake garin wudil jihar Kano . Kuma yana da burin ƙwarewa a aikin jarida.

Za'a iya samunsa a dandalin sada zumunta na twitter @ahmadyusufmuha77.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: