Jerin jihohi 16 da suka samu kasonsu na rigakafin COVID-19 da adadin da suka samu

Jerin jihohi 16 da suka samu kasonsu na rigakafin COVID-19 da adadin da suka samu

Jihohi daban-daban a fadin tarayya sun kaddamar da yiwa al'ummarsu rigakafin cutar Korona.

Kawo yanzu, jihohi 16 cikin 36 na kasar sun samu nasu kason na rigakafi daga gwamnatin tarayya.

A cewar jaridar Leadership, jihohi 16 sun karbi jimillan rigakafin Oxford-AstraZeneca 1,871,050.

Jerin jihohi 16 da suka samu kasonsu na rigakafin COVID-19 da adadin sa suka samu
Jerin jihohi 16 da suka samu kasonsu na rigakafin COVID-19 da adadin sa suka samu Photo credit: @dabiodunMFR, @GboyegaOyetola, @kfayemi
Asali: Twitter

DUBA NAN: Gwamnatin Bayelsa ta kafa dokar hana makiyaya kiwo a faɗin jihar

Ga jerin jihohin da suka samu rigakafin da adadin da suka samu:

1. Jihar Benue - 78,108,

2. Jihar Borno - 75,510

3. Jihar Ekiti - 52,000

4. Jihar Jigawa - 68,000

5. Jihar Nasarawa - 61,000

6. Jihar Niger - 74,110

7. Jihar Ondo - 73, 570

8. Jihar Cross River - 50,840

9. Jihar Osun - 64,240

10. Jihar Ebonyi - 42,090

11. Jihar Plateau - 105,600

12. Jihar Ogun - 100,000

13. Jihar Adamawa - 59,280

14. Jihar Lagos - 507,000

15. Jihar Kano - 200,000

16. Jihar Kaduna - 180,000

KU KARANTA: Gwamnan Neja ya bada umurnin rufe dukkan makarantun sakandaren gwamnatin jihar

Gabanin yanzu, gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya ce sam shi ba zai karbi rigakafin COVID-19 ba saboda ba ya bukata.

Ya bayyana cewa shi bai da wata matsalar lafiya da ke bukatar ya yi rigakafin.

Kun ji cewa gwamnatin jihar Kano ta samu karban rigakafin AstraZeneca na cutar Korona.

Kwamishanan kiwon lafiya na jihar, Aminu Tsanyawa, ne ya karbi rigakafin ranar Talata a tashar jirgin Malam Aminu Kano madadin gwamnan jihar.

Tsanyawa ya ce gwamnatin jihar za ta fara mayar da hankali da jami'an kiwon lafiya wajen basu rigakafin kafin yiwa gamagarin jama'a.

Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin uku yanzu tare da shararriyar jarida Legit.

Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss.

Asali: Legit.ng

Online view pixel