Ba a biya kudin fansa wajen fito da ‘Yan makarantar Jangebe ba inji Gwamnan Zamfara

Ba a biya kudin fansa wajen fito da ‘Yan makarantar Jangebe ba inji Gwamnan Zamfara

- Gwamnan jihar Zamfara ya bayyana yadda aka bi aka ceto Daliban GSS Jengebe

- Bello Matawalle ya ce tsofaffin ‘Yan bindiga su ka taimaka aka kubuto da yaran

- Dalibai 279 aka kubutar bayan sun shafe kwanaki hudu a hannun ‘Yan bindiga

Gwamnan jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawalle ya bayyana yadda aka bi aka ceto ‘daliban makarantar mata ta Jengebe da aka sace a makon jiya.

Mai girma gwamna Muhammad Bello Matawalle ya ce tsofaffin ‘yan bindigan da su ka tuba ne su ka yi uwa da makarbiya wajen fito da wadannan yaran.

A cewar gwamnan na jihar Zamfara, ko sisi gwamnati ba ta ba ‘yan bindigar da su ka dauke ‘yan matan ba.

Gwamna Bello Matawalle wanda ya yi wa ‘yan bindiga afuwa, ya ce tubabban masu laifin da ke jihar ne su ka ceto wadannan ‘dalibai daga hannun miyagu.

Kara karanta wannan

‘Yan Bindiga Sun Halaka Dan Sanda Da Wasu 22 Sannan Suka Kona Gidaje 50 A Wata Jahar Arewa

KU KARANTA: Masu satar mutane sun yi cinikin kudin fansar Biliyan 10 a 2021

Gwamnan ya bayyana wannan ne a lokacin da BBC Hausa ta yi hira da shi da safiyar ranar Talata, 2 ga watan Maris, 2021, bayan an kubuto da duka ‘yan matan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bello Matawalle ya ce wasu ‘yan bindiga su kusan 30 da su ka tuba, su ka ajiye makaman yaki ne su ka taimaka wa gwamnati wajen ceto ‘daliban nan su 279.

Kamar yadda gwamna Matawalle ya yi bayani, duka yaran da aka ceto su na cikin koshin lafiya. A lokacin ya yi alkawari za a hada kowa da iyayensa daga baya.

Har ila yau, gwamnan ya karyata rade-radin da ake yi na cewa wasu daga cikin ‘daliban da aka sace sun yi batan-dabo ko su na nan a hannun ‘yan bindigan.

Kara karanta wannan

‘Dan Takaran Jam’iyyar NNPP ya Raba Kayan Tallafin Ga Wadanda Masifa ta Auka Masu

Ba a biya kudin fansa wajen fito da ‘Yan makarantar Jangebe ba inji Gwamnan Zamfara
Daliban GSS Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

KU KARANTA: Mun ci duka a hannun wadanda suka sace mu - Daliban Kagara

Matawalle ya ce tun asali ‘dalibai 279 aka dauke daga wannan makarantar gwamnati kamar yadda rajista ta nuna, akasin rahoton da aka ji na cewa su 217 aka sace.

Watanni biyu da su ka wuce ne 'yan bindiga su ka sace wasu 'yan makaranta a jihar Katsina.

Daga baya kungiyar Boko Haram ta fito ta na bada sanar cewa ita ce ta sace wadannan dalibai fiye da 300 daga makarantar sakandaren kimiyya da ke Kankara.

Kamar yadda HumAngle ta rawaito, gwamnatin Katsina ta ce 'yan bindiga ne su ka dauke yaran.

M. Malumfashi ma'aikacin jaridar Legit.ng ne wanda ya shafe kusan shekaru 5 ya na wannan aiki. Ya yi Digirin farko a ilmin komfuta da Digirgir a harkar bayanai, kuma ya na Digirgir a ilmin aikin jarida.

Malumfashi ya kan buga labarai, ya yi rubuce-rubuce a harkar siyasa, wasanni da addini. Ya yi rubuce-rubuce barkatai a gidajen jaridun Najeriya.

Kara karanta wannan

Ziyarar da Peter Obi Ya Kai wa Dr. Ahmad Gumi ta Jawo Masa Bakin jinin Magoya baya

A bibiye shi a Twitter @m_malumfashi

Asali: Legit.ng

Online view pixel