Ban taba karbar ko sisi ba a shekaru 8 da nayi a gwamnan jiha, Tsohon gwamna

Ban taba karbar ko sisi ba a shekaru 8 da nayi a gwamnan jiha, Tsohon gwamna

- Tsohon gwamnan jihar Osun kuma ministan Buhari ya ce bai taba karbar ko sisi ba a matsayin albashi lokacin yana gwamna

- Ogbeni Rauf Aregbesola ya musanta labarin da ke yawo cewa ya samu albashin watanni 96 a sirrance kafin karewar wa'adinsa

- A cewarsa, gwamnati ta samar masa da wurin zama, abinci, sufuri da sauransu, don haka baya bukatar albashi

Tsohon gwamnan jihar Osun kuma ministan cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola a ranakun karshen mako ya musanta labarin da ke yawo na cewa ya samu albashinsa na watanni 96 a sirrance a lokacin da yayi shugabancin jihar.

Ya kwatanta rahoton da labarin kanzon kurege wanda aka hada shi domin zubar da nagartar Ogbeni Rauf Aregbesola.

A wata takarda da hadimin Aregbesola na yada labarai, Soka Fasure ya fitar, ya ce rahoton da ake yaduwa a yanar gizo ya saba dokokin jaridanci, The Nation ta wallafa.

KU KARANTA: Da duminsa: 'Yan bindiga sun sako 'yan makarantar Kagara, amma akwai wasu kalubale

Ban taba karbar ko sisi ba a shekaru 8 da nayi a gwamnan jiha, Tsohon gwamna
Ban taba karbar ko sisi ba a shekaru 8 da nayi a gwamnan jiha, Tsohon gwamna. Hoto daga @Thenation
Asali: Twitter

Kamar yadda takardar tace, marubucin ya yi ikirarin karya na cewa ministan cikin gida kuma tsohon gwamnan jihar Osun, Ogbeni Rauf Aregbesola, wurin karshen mulkinsa ya samu dukkan albashinsa a sirrance, akasin yadda yayi ikirari.

"Rahoton dukkan shi labarin kanzon kurege ne, labarin bogi kuma mara amfani a jaridance."

Hadimin ya ce: "Bari in sake bayyanawa, Ogbeni Aregbesola bai taba karbar albashi ba a shugabancin jihar Osun da yayi na shekaru takwas.

"Dalilansa sune gwamnati ta samar da wurin zama, tsaro, sufuri, abinci da sauran ababen amfanin rayuwa. Don haka babu bukatar a biya shi wasu kudade.

"Ya kara da yin bayanin cewa dukkan 'ya'yansa sun girma kuma sun kammala karatu don haka babu bukatar biya musu kudin makaranta. A don haka ya sadaukar da albashinsa ga gwamnatin jihar.

"Marubucin rahoton ya yi ikirarin cewa ya samu bayanan ne daga wasu jami'an gwamnati amma ba a samar da shaida ba."

KU KARANTA: Caccakar Buhari: DSS ta cafke hadimin Ganduje, Dawisu, bayan yace APC ta gaza

A wani labari na daban, a wani lamari mai taba zuciya a Najeriya, wasu 'yan bindiga sun bindige wasu mutane 22 a jihar Zamfara.

A ranar Alhamis, 25 ga watan Fabrairun 2021, 'yan bindiga sun kai samame inda suka kashe a kalla mtum 22, Daily Trust ta wallafa.

Kamar yadda aka gani, lamarin ya faru a wani wurin hakar zinari da ke kusa da Sabuwar Tunga a kauyen Dankurmi da ke karamar hukumar Maru.

Aisha Khalid ma'aikaciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018.

Ta kwashe shekaru biyu tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu.

Za a iya bibiyar Aisha a shafinta na Twitter @DiyarKatsinawa

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel