Sanusi ya bukaci gwamnati ta kayyadewa 'yan Najeriya yawan iyalin da za su haifa

Sanusi ya bukaci gwamnati ta kayyadewa 'yan Najeriya yawan iyalin da za su haifa

- Tubabben sarkin Kano, Sanusi II ya bukaci gwamnati da ta saka dokar kayyade yawan iyali

- Tsohon shugaban babban bankin ya ce hakan ne kawai zai kawo daidaituwar yawan 'yan Najeriya

- Muhammadu Sanusi ya ce ba Musulunci bane haifar yaran da ba za a iya kula da su da kyau ba

Tsohon sarkin Kano, Muhammad Sanusi II yayi kira ga gwamnati da ta saka tsauraran dokoki da za su daidaita hauhawar yawan jama'a a kasar nan.

Sanusi wanda yayi magana a ranar Laraba yayin wani taro a Legas, ya ce ya dace jama'a su dinga haifar yaran da za su iya kula da su, Daily Trust ta wallafa.

Kamar yadda tsohon gwamnan babban bankin Najeriya yace, abubuwan da ke bayyana a halin yanzu sun nuna cewa gwamnati ba za ta iya samar da dukkan ababen more rayuwa da ake bukata ba.

KU KARANTA: Da duminsa: COAS na Goodluck Jonathan ya sauya sheka, ya koma jam'iyyar APC

Sanusi II: Ba Musulunci bane haifar 'ya'yan da ba za a iya kula da su ba
Sanusi II: Ba Musulunci bane haifar 'ya'yan da ba za a iya kula da su ba. Hoto daga @daily_trust
Asali: Twitter

Sanusi ya kushe yadda ake haihuwa a kasar nan ba tare da karfin kula da yaran ba, wanda yace hakan ba daidai bane ko a addinin Musulunci.

Ya ce: "Yadda jama'a ke auren duk yawan matan da suke so ba tare da wata dokar da ta gindaya yawan yaran da za a haifa ba bai dace ba ko a Musulunci.

"Ban san dalili ba amma akwai doka a Musulunci da ta hana tara iyali ba tare da kayyade su ba. Babu wani tabbacin cewa za a iya kula dasu ba tare da an yi watsi da dawainiyarsu ba."

KU KARANTA: Yara 7 sun samu rauni bayan 'abu mai fashewa' ya tarwatse suna wasa dashi a Kaduna

A wani labari na daban, tsohon shugaban majalisar dattawa, Dr Bukola Saraki ya bayyana cewa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ba zai samu damar tsayawa takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar APC ba a zaben shugaban kasa 2023.

Saraki ya bayyana hakan a ranar Talata bayan ya tasa 'yan kwamitin sasanci na jam'iyyar PDP zuwa gidan tsohon shugaban kasar dake Abuja.

A taron da suka yi da Jonathan an samu labarai iri-iri na batun shugabannin jam'iyyar APC da tsohon shugaban kasar wanda ya janyo cece-kuce iri-iri a kafafen sada zumuntar zamani, inda har wasu suke zaton APC za ta tsayar da Jonathan takara a 2023.

Aisha Khalid ma'aikaciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018.

Ta kwashe shekaru biyu tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu.

Za a iya bibiyar Aisha a shafinta na Twitter @DiyarKatsinawa

Asali: Legit.ng

Online view pixel