Babu hujjar kimiyya mai nuna ganyen Bay da Kanunfari na maganin ciwon gabbai

Babu hujjar kimiyya mai nuna ganyen Bay da Kanunfari na maganin ciwon gabbai

- Wasu likitoci sun yi fata-fata da da'awar cewa ganyen Bay da kanunfari na maganin ciwon gabobi

- Sun bayyana hakan a matsayin barazana ga lafiya idan mutum bai kula da shan irin wadannan magunguna ba

- Sun kuma bayyana cewa, babu magani takamaimai dake magance ciwon gabobi a likitance, sai dai ya rage

Wani marubuci ya yi iƙirarin cewa cakuda ganyen bay da kanunfari shine mafita ga ciwon gabobi kuma yana ba da shawarar tsabtace kayan ƙanshi a cikin ruwan zafi a sha kamar shayi sau biyu a rana, Daily Trust ta ruwaito.

Amma shin da gaske wannan hadin yana maganin ciwon gabobin?

Rashin jin daɗi, radadi, da ciwon gabobi da sauran sassan jiki yana da dalilai masu yawa, amma ɗayan da ya fi yawa shine amosanin gabobi.

KU KARANTA: Kada ku tausayawa 'yan ta'adda, IGP ya fadawa rundunar 'yan sanda

Babu wata hujjar kimiyya mai nuna cewa ganyen Bay da Kanunfari na maganin ciwon jiki
Babu wata hujjar kimiyya mai nuna cewa ganyen Bay da Kanunfari na maganin ciwon jiki Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Ba za a iya kawar da ciwon gabobi ba galibi, amma ana iya rageshi ta amfani da magungunan rage radadi ko magungunan kwayoyin cuta marasa amfani don rage ciwo, da kuma kumburin jiki.

"A cikin aikin likitanci, mun fi son amfani da magungunan da aka gwada da kuma aka tabbatar da magunguna," in ji Basden Onwubere, Farfesa a fannin ilimin likitanci a jami'ar Najeriya Nsukka (UNN), ya fada wa Africa Check.

Onwubere ya kara da cewa "Abubuwan da aka samu a dabi'ance na iya zama marasa illa, amma illolin likitanci na bukatar lamuran yau da kullun na kimiyya."

Ikpeme Ikpeme, farfesa a fannin ilimin kasusuwa da tiyata a Jami’ar Calabar, shi ma ya fada wa Africa Check cewa bai ci karo da wani bincike da ya shafi da’awar ba game da ganyen bay da kanunfari ba, kuma ya kara da cewa ya kamata a yi watsi da shi.

Ya ce, "Ziyarci likita idan kana da kalubale na kiwon lafiya."

KU KARANTA: PDP ta yi Allah-wadai game da rikicin Hausawa da Yarbawa a Ibadan

A wani labarin, Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum, ya amince da biyan naira miliyan 13.9 da kyautar mota ga wani likita mai shekaru 65 daga jihar Ogun.

Likitan shine wanda ke zaune a cikin Babban Asibitin da ke Monguno kuma ya ci gaba da kula da marasa lafiya har ma lokacin da garin ya fuskanci mummunar barazanar kungiyar Boko Haram, The Nation ta ruwaito.

Salisu Ibrahim, mai rubutu a masana'antar Legit.ng Hausa da ya fara aiki a baya-bayan nan. Ya kware wajen kawo rahotanni na siyasa, kimiyya, al'adu da sauran lamurran yau da kullum.

Ya yi karatun diploma a fannin karantar da turanci a jami'ar Ahmadu Bello, ya kuma karantar na tsawon shekaru 7.

A halin yanzu yana zangon karshe na karatun digiri a fannin ilimin fasahar sadarwa a International Open University.

Ku bibiyi shafinsa na twitter a @therleez

Asali: Legit.ng

Online view pixel