Saboda kariya nace makiyaya su dinga yawo da AK47, Gwamnan Bauchi ya kare kansa

Saboda kariya nace makiyaya su dinga yawo da AK47, Gwamnan Bauchi ya kare kansa

- Gwamnatin jihar Bauchi ta kara haske a kan kalaman gwamnan jihar inda yace makiyaya su dinga yawo da AK-47

- A wata takarda da hadimin Gwamna Mohammed ya fitar, ya ce ba a fahimci tsokacin da ubangidansa yayi bane da kyau

- Mukhtar Gidado ya ce Gwamna Mohammed ya sanar da hakan ne da nufin masu ruwa da tsaki su hana tabarbarewar lamurran

Gwamnatin jihar Bauchi ta kara haske a kan jawabin Gwamna Bala Mohammed inda yace makiyaya su dinga yawo da AK-47 domin baiwa kansu kariya.

A wata takarda da aka fitar a ranar Lahadi 14 ga watan Fabrairu, Mukhtar Gidado wanda babban mai baiwa gwamnan shawara ne a kafafen sada zumunta ya ce ba a fahimci tsokacin ubangidansa bane, The Punch ta wallafa.

Idan za a tuna, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya bukaci makiyaya su dinga yawo da AK-47 domin shawo kan matsalar satar shanunsu da ake yi.

KU KARANTA: Sojin Najeriya sun sheke Abul-Bas da Ibn Habib, manyan kwamandojin Boko Haram

Saboda kariya nace makiyaya su dinga yawo da AK47, Gwamnan Bauchi ya kare kansa
Saboda kariya nace makiyaya su dinga yawo da AK47, Gwamnan Bauchi ya kare kansa. Hoto daga @Vangauradngrnews
Asali: UGC

Amma a martanin da gwamnan yayi, Gidado ya ce ba a fahimce shi bane kuma ba yana nufin goyon bayan 'yan ta'addan makiyaya bane.

"Gwamnan zai so a gane cewa yana so ne ya janyo hankalin masu ruwa da tsaki da su yi kokarin hana hauhawar rikici kamar dai yadda duk wani mai kishin kasa zai yi. A kuma gujewa duk wani hari da zai iya jefa kasar nan cikin halin rikici."

KU KARANTA: 'Yan bindiga sun sheke Ali Bahago, wani shugaban 'yan sa kai a Katsina

A wani labari na daban, Ahmad Gumi, babban malamin addinin nan, ya ce 'yan bindiga suna tattara kudaden da suke amsa a matsayin kudaden fansa daga hannun jama'a don siyan makami mai linzami na harbo jiragen saman.

Gumi ya samu ganawa da wasu 'yan bindiga a dajin jihar Zamfara. Bayan ganawar ne ya bukaci gwamnatin tarayya ta yafe musu ta kuma taimaka musu, don sun rasa shanunsu sakamakon rikicin nan.

A tattaunawar da The Punch suka yi da Gumi, ya ce da yuwuwar ta'asar 'yan bindiga ta karu idan gwamnati bata yi wani abu ba a kai.

Aisha Khalid ma'aikaciyar jaridar Legit.ng ce mai fatan shahara. Ta samu digirinta na farko a jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria a shekarar 2018.

Ta kwashe shekaru biyu tana rubutu a fannonin siyasa, nishadi, tsegumi da sauransu.

Za a iya bibiyar Aisha a shafinta na Twitter @DiyarKatsinawa

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel