Yanzu Yanzu: Amurka ta goyi bayan Okonjo-Iweala ta jagoranci WTO

Yanzu Yanzu: Amurka ta goyi bayan Okonjo-Iweala ta jagoranci WTO

- Kasar Amurka ta goyi bayan Okonjo-Iweala domin aikin Kungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO)

- Ku tuna cewa tsohuwar gwamnatin Trump ta ki mara mata baya saboda wasu dalilai

- Yan Amurka sun jinjina mata kan kasancewa da tarin sani a fannin tattalin arziki da diflomasiyyar kasa da kasa

Duk da cewar gwamnatin Shugaba Trump ta ki lamuncewa takarar Ngozi Okonjo-Iweala don jagorantar Kungiyar Cinikayya ta Duniya (WTO), tsohuwar ministar kudin ta Najeriya ta samu muradinta.

Musamman, gwamnatin Joe Biden a ranar Juma’a, 5 ga watan Janairu, ta bayar da cikakken goyon bayanta a kudin Okonjo-Iweala.

KU KARANTA KUMA: Rikicin makiyaya da manoma: Tinubu ya yi shiru ne saboda baya so ya rasa hulunansa, Sani

Yanzu Yanzu: Amurka ta goyi bayan Okonjo-Iweala ta jagoranci WTO
Yanzu Yanzu: Amurka ta goyi bayan Okonjo-Iweala ta jagoranci WTO Hoto: @NOIweala
Asali: UGC

Ku tuna cewa Trump ya ki amincewa da ita duk da goyon bayan da ta samu da sauran kasashe da dama.

KU KARANTA KUMA: Ba za mu bari mutum 1 ya jawo mana rikici ba, Ganduje ya bayyana dalilin haramta wa Sheikh Kabara yin wa’azi

A cewar wakilan kasuwanci na Amurka, tana da tarin ilimi a fannin tattalin arziki da diflomasiyyar kasa da kasa.

Bugu da kari, yan Amurkan sun yaba mata a kan “nuna kwarewa wajen kula da babban kungiyar kasa da kasa.”

A baya mun ji cewa wasu shugabanni a Amurka har da Joseph Stiglitz, sun aika wasika ga Joe Biden, suna rokon shi ya goyi bayan takarar Dr. Ngozi Okonjo-Iweala a kungiyar WTO.

A wata budaddiyar wasika da manyan suka rubuta wa sabon shugaban kasar, sun ba Jode Biden shawarar cewa za a yaba idan ya ba Ngozi Okonjo-Iweala goyon baya.

Kamar yadda jaridar The Cable ta fitar da rahoto, ana ganin cewa Duniya za ta yi wa Biden kallon ya na jawo kowa a jika idan ya goyi bayan tsohuwar Ministar Najeriyar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel