Dalilin da yasa Buhari ya sallami hafsoshin tsaro, Fadar shugaban kasa

Dalilin da yasa Buhari ya sallami hafsoshin tsaro, Fadar shugaban kasa

- Fadar shugaban kasa ta ce ba saboda gazawa bane aka ssallami tsoffin hafsoshin tsaro ba

- An sallamesu ne saboda ana bukatar sabbin jini kuma da sabbin dabarun yaki

- Buhari ya jinjinawa tsoffin hafsoshin tsaron ta yadda suka bautawa kasar nan

Fadar shugaban kasa a ranar Talaa ta ce abinda yasa aka sallami hafsoshin tsaro a yau ba saboda sun gaza bane. Ta kara da cewa an yi hakan ne a wannan lokacin domin kara karfi a fannin yaki da ta'addanci tare da shawo kan matsalolin tsaro a kasar nan.

Femi Adesina, mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman a fannin yada labarai, ya sanar da hakan a wata zantawa da yayi da Channels TV a kan siyasa kuma Punch ta kiyaye.

"Abinda yasa suka tafiya a yau ba yana nufin sun gaza bane. A gaskiya ba hakan bane. Kawai ana son sabbin jini ne da kuma sabbin dabarun yaki a kasar nan," yace yayin da yake sanar da jinjinar da Buhari yayi wa tsoffin shugabannin tsaron.

KU KARANTA: Ba ki cancanci a aure ki ba idan namiji yana magana kina mayarwa, Budurwa ga tsagerun mata

Dalilin da yasa Buhari ya sallami hafsoshin tsaro, Fadar shugaban kasa
Dalilin da yasa Buhari ya sallami hafsoshin tsaro, Fadar shugaban kasa. Hoto daga @MobilePunch
Asali: Twitter

"A takardar da shugaban kasar ya fitar a yau Talata, ya jinjinawa hafsoshin tsaron da suka tafi a kan gudumawar da suka bada wurin tsaron kasar nan. Ya gamsu da ayyukansu ba kadan ba.

“Wadannan da suke tafiya a yau sun kasance a kujerunsu na tsawon shekaru biyar da watanni biyar. Lamarin na yin abinda ya dace ne a lokacin da ya dace," Adesina ya kara da cewa.

KU KARANTA: Kafintan da matansa suka haifa yara 4 a mako 3 yace burinsa ya haifa yara a kalla 40

A wani labari na daban, jam'iyyar PDP ta kwatanta canja tsofaffin shugabannin tsaro da shugaba Muhammadu Buhari yayi a matsayin makararren mataki, don jama'a sun riga sun cutu, Daily Trust ta ruwaito.

PDP ta bukaci a yi gaggawar bincike akan yadda tsofaffin shugabannin tsaron suka tafiyar da ayyukansu lokacin da suke kan kujerunsu, saboda tana zargin suna da hannu dumu-dumu akan satar kudaden da aka ware musamman don tabbatar da walwalar rundunoni a filayen daga.

A wata takarda ta ranar Talata, sakataren yada labaran jam'iyyar, Kola Ologbondiyan ya ce "Daga baya kenan, sadaka da karuwa. A cewarsa sun riga sun janyo rikicewar kasa da asarar rayuka."

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel