Gwamnatin tarayya tace ta shiryawa 'yan N-Power goma na arziki

Gwamnatin tarayya tace ta shiryawa 'yan N-Power goma na arziki

- Gwamnatin tarayya ta shirya yiwa 'yan N-Power alheri a sabon tsarin NEXIT

- Gwamnati ta bayyana cewa a shirin nata za ta dauki wasu aiki na dindindin

- Wasu kuwa zasu mori bashi a karkashin tsarin GEEP da babban bankin tarayya ke gudanarwa

Masu cin gajiyar N-Power, wadanda suka kammala shirin aikin na shekaru biyu, yanzu za su sami damar samun aikin dindindin ko damar kasuwanci, in ji Gwamnatin Tarayya.

Wannan wani bangare ne na sabuwar kokarin gwamnati kan fita daga tsarin N-power.

Tsarin an yi shine ga dukkan 'yan tsarin A da B na shirin N-Power.

Ministar Harkokin Jin Kai, da Ci Gaban Jama'a, Sadiya Farouq, ce ta bayar da sanarwar a ranar Laraba, The Nation ta ruwaito.

Ta yi magana ne a nazarin shekara-shekara na 4 na Tsarin Ciyarwar Makaranta na Gida (NHGSFP).

KU KARANTA: Masu garkuwa da mutane sun kame wanda ya kawo kudin fansar 'yan uwansa

Gwamnatin tarayya tace ta shiryawa 'yan N-Power goma na arziki
Gwamnatin tarayya tace ta shiryawa 'yan N-Power goma na arziki Hoto: Legit.ng
Asali: UGC

A karkashin shirin, masu cin gajiyar 200,000 za su tsunduma a matsayin masu gudanar da aiyukan hada-hadar kudi a karkashin Shared Agent Network Fadada Facility (SANEF) da Babban bankin Najeriya (CBN) ke gudanarwa.

“An kammala shirye-shirye don sauyawar N-power shirin A da B ta hanyar kirkirar hanyar NEXIT, wanda zai ba wa wadanda suka zabi shiga rajista domin samun wasu damar tsarin karfafawa na gwamnati."

Sadiya ta ce "Ana sa ran shigar da tsarin kula da cin gajiyar NSIP a shekarar 2021. Zai iya samun damar gudanar da biyan kudi, magance korafe-korafe da inganta yada labarai."

Gwamnatin ta ce wasu masu cin gajiyar 30,000 tuni sun kasance a cikin wani shirin bunkasa tattalin arziki.

Sauran za su sami zaɓi na cin gajiyar rancen ƙananan Masana'antu na Gwamnatin da kuma Karfarfafawa (GEEP).

KU KARANTA: Babban hadari ne gwamnati ta ci bashin N9.8tn - Fitch Ratings

A wani labarin. Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo (SAN) ya ce hangen nesan gwamnatin Buhari na fitar da akalla ‘yan Najeriya miliyan 20 daga kangin talauci a cikin shekaru biyu masu zuwa yanzu ya kusa.

Farfesa Osinbajo ya bayyana hakan ne a ranar Talata, 19 ga watan Janairu a Abuja yayin fara shirin fara hada hadar kudade da gwamnatin tarayya ta fara.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel