Sojojin Najeriya sun yi ruwan bama-bamai kan maboyar ‘yan ta’adda a Borno
- Rundunar sojin sama na Najeriya ya samu damar halaka 'yan ta'adda a borno
- Sojoijn sun kai harin bayan samun bayanan sirri ingattace daga majiya mai tushe
- Harin ya jawo ruguje mafakar 'yan ta'addan tare da kashe da yawa a cikinsu
Hedikwatar tsaro ta ce rundunar sojin sama ta Operation Lafiya Dole ta rusa wasu mafakar ‘yan ta’addan, inda suka kashe 'yan ta'addan da yawa a wurare biyu a Borno.
Jami'in yada labarai na bangaren yada labarai na tsaro, John Enenche, a wata sanarwa a ranar Lahadi, ya ce an kai hare-haren ne a ranar Asabar a garuruwan Kote Kura da Bulama Isamari da ke Borno.
KU KARANTA: Boko Haram sun sace ma’aikacin Majalisar Dinkin Duniya a hanyar Maiduguri zuwa Damaturu
Mista Enenche ya ce, rundunar ta Air Force ta yi amfani da jiragen yaki da kuma jiragen yaki masu saukar ungulu bisa ingantattun bayanan sirri.

Source: Facebook
Ya ce bayanan sirrin sun gano cewa 'yan ta'addan Boko Haram sun kafa sansanoni a tsakanin matsugunan biyu inda suke ajiye kayan aikin su tare da shiryawa da kuma kai hare-hare.
A cewarsa, a saman Kote Kura, wani yanki a yankin Bama, jirgin saman NAF ya yiwa 'yan ta'adda da dama dirar mikiya a yankin da aka nufa.
“Harin ya kai ga kawar da yawancinsu tare da lalata gine-gine da wuraren adana kayan aiki, an ga wasu suna cikin wuta.
KU KARANTA: ‘Yan sanda sun kame wadanda ake zargi da yin garkuwa da Bishop din Katolika na Owerri
"A daidai wannan hanyar, a Bulama Isamari, a cikin Timbuktu Traingle, jirgin NAF ya juyo da niyyar aiwatar da abin da ya sa a gaba, ya zira kwallaye daidai wanda hakan kuma ya haifar da kawar da 'yan ta'adda da dama," in ji shi.
A wani labarin, A ƙalla sama da fararan hula 70 ne aka kashe a wasu tagwayen hare-hare da ake zargin yan kungiyar Boko Haram ne suka kai kan wasu ƙauyuka biyu dake ƙasar Nijar kusa da iyaka da kasar Mali.
Kimanin mutum 50 ne aka kashe a ƙauyen Tchombangou sannan 17 suka ji mummunan rauni kamar yadda wani jami'in tsaro ya tabbarwa Reuters ya kuma nemi da a sakaye sunansa, kamar yadda TheCable ta rawaito.
Wata majiya daga wani jami'in harkokin cikin gida na ƙasar ta Nijar da shima ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da an kashe sama da kimanin mutum 30 a Zaroumdareye.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng