Diyar tsohon shugaban majalisa, David Mark ta koma APC

Diyar tsohon shugaban majalisa, David Mark ta koma APC

- Diyar tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata David Mark da mogaya bayanta sun fice daga jam'iyyar APGA ta koma APC

- Blessing Mark, sanata mai wakiltar Otukpo/Ohimini ta shawarci sauran 'yan APGA da PDP a mazabar Benue ta Kudu su shigo APC

- A cewar Blessing, jam'iyyar PDP ta mutu har an birne ta don haka kowa ya shigo APC don ita zata karbe mulki a jihar

Blessing Onu Mark, diyar tsohon shugaban majalisar dattawa David Mark, a karshen mako ta yi wa daruruwan mambobi da magoya bayan jam'iyyun APGA da PDP jagora zuwa jam'iyyar APC a jihar Benue.

Blessing, yar majalisar tarayya ce da ke wakiltar mazabar Otukpo/Ohimini na jihar Benue.

Diyar tsohon shugaban majalisa, David Mark ta fice daga PDP ta koma APC
Diyar tsohon shugaban majalisa, David Mark ta fice daga PDP ta koma APC. Hoto: @TheNationNews/Uja Emmanuel
Asali: Twitter

The Nation ta ruwaito cewa mambobin wasu jam'iyyun siyasa a jihar suma sun sauya sheka zuwa jam'iyyar ta APC.

DUBA WANNAN: Hotuna: Ganduje ya tafi ta'aziyya Danbatta, ya bada N1.6m ga iyalan mutum 16 da suka rasu

Ta lashe zaben kujerar wakilcin Otukpo/Ohimini a karkashin inuwar jam'iyyar APGA, inda ta kayar da 'yan takarar PDP da APC a 2019.

A ranar Asabar, ta sauya sheka zuwa jam'iyyar APC tare da magoya bayan ta a mazabar Benue ta Kudu tare da kananan hukumomi tara.

Da ta ke jawabi yayin taro a Otukpo hedkwatan mazabar Benue ta Kudu, Blessing ta bayyana cewa PDP ta mutu an kume birne ta a Zone C don haka ta bukaci sauran yan PDP su koma APC.

KU KARANTA: Masoyin Buhari ya ce shugaban kasar ya yi murabus bayan sace yan uwansa a Katsina

Ta ce APC ce za ta karbe mulki a Jihar Benue, "don itace jam'iyyar da kowa ya dace ya shiga."

Daruruwan mutane daga wasu jam'iyyun sun shiga APC sannan an basu katin kasancewa dan jam'iyya.

A wani labarin daban, mashahurin attajirin Brazil dan asalin kasar Lebanon Joseph Safra, ya rasu ranar Alhamis ya na da shekara 82, a cewar bankinsa.

Safra, wanda kiyasin dukiyar ya kai kimanin $23.2 biliyan, wanda ya zo na 63 cikin jerin masu kudin duniya da mujallar Forbes ta fitar.

An haife shi a 1938 ga wasu iyalai Yahudawa a Beirut, yayi hijira shi da Iyalan sa zuwa Brazil, inda mahaifin sa ya samar da inda ake kira Banco Safra.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel