Mawallafin Jaridar Leadership, Sam Nda-Isaiah ya rasu

Mawallafin Jaridar Leadership, Sam Nda-Isaiah ya rasu

- Mawallafin Jaridar Leadership Newspaper, Mista Sam Nda-Isaiah ya riga mu gidan gaskiya

- Ya rasu ne misalin ƙarfe 10 na daren ranar Juma'a bayan ya koka cewa baya jin daɗin jikinsa

- Nda-Isiah ya hallarci taron kungiyar masu jaridu, NPAN, a Legas a ƙarshen makon da ta gabata

Allah ya yi wa mawallafin Jaridar Leadership, Mista Sam Nda-Isaiah rasuwa yana da shekaru 58 a duniya.

Majiyoyi sun bayyana wa The Nation cewa marigayin ya rasu misalin ƙarfe 10 na daren ranar Juma'a bayan ya koka kan cewa baya jin daɗin jikinsa.

Mawallafin Jaridar Leadership, Sam Nda-Isiah ya rasu
Mawallafin Jaridar Leadership, Sam Nda-Isiah ya rasu. Hoto: @SamNdaIsaiah
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Zahra Buhari ta taya mijinta murnar zagayowar ranar haihuwarsa da kalaman soyayya

Nda-Isiah ya hallarci taron kungiyar masu jaridu ta Najeriya, NPAN, a jihar Legas a ƙarshen mako.

Marigayin wanda haifaffen jihar Niger ne ya yi karatun digiri a fannin kimiyyar magunguna a Jami'ar Ife.

Ya kuma taɓa neman tikitin takarar kujerar shugabancin ƙasa a jam'iyyar All Progressives Congress, APC.

Wani daga cikin iyalansa ya shaidawa wakilin jaridar Punch a wayar tarho cewa:

"Eh, da gaske ne. Yanzu aka sanar da ni."

KU KARANTA: 'Yan bindiga sun kashe Kanawa 16 a titin Kaduna zuwa Abuja

A lokacin hada wannan rahoton, babu sanarwar rasuwarsa a shafin jaridar ta Leadership.

Sai dai wasu daga cikin fitattun mutane ciki har da kakakin Shugaba Muhammadu Buhari, Garba Shehu ya yi ta'aziyar rasuwarsa.

An haife shi a shekarar 1962 a Minna, Jihar Niger. Mista Nda Isaiah kuma yana da sarautar Kakakin Nupe a jihar Niger.

A wani labarin daban, mashahurin attajirin Brazil dan asalin kasar Lebanon Joseph Safra, ya rasu ranar Alhamis ya na da shekara 82, a cewar bankinsa.

Safra, wanda kiyasin dukiyar ya kai kimanin $23.2 biliyan, wanda ya zo na 63 cikin jerin masu kudin duniya da mujallar Forbes ta fitar.

An haife shi a 1938 ga wasu iyalai Yahudawa a Beirut, yayi hijira shi da Iyalan sa zuwa Brazil, inda mahaifin sa ya samar da inda ake kira Banco Safra.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel