Majalisa bata da ikon tilasta wa Buhari ya bayyana gabanta, in ji Malami

Majalisa bata da ikon tilasta wa Buhari ya bayyana gabanta, in ji Malami

- Atoni janar na Najeriya, Abubakar Malami ya ce Majalisar Tarayya bata da ikon tilasta wa shugaban kasa gurfana gabanta

- Malami ya yi wannan jawabin ne kan gayyatar da majalisar wakilai ta yi wa Buhari kan taɓarbarewar tsaro

- Ana tsammanin shugaban kasar zai amsa kirar majalisar ranar Alhamis amma yanzu babu tabbas hakan zai faru

Abubakar Malami, Atoni Janar kuma ministan Shari'a na ƙasa ya ce a ƙarƙashin doka majalisa bata da ikon tilasta wa shugaba Muhammadu Buhari ya gurfana gabanta kamar yadda The Punch ta ruwaito.

A makon da ta gabata, majalisar wakilai na tarayya ta cimma matsayar gayyatar shugaban ƙasar don mata bayani kan taɓarbarewar tsaro a ƙasar a wani zama da tayi karkashin jagoracin kakakin majalisa Femi Gbajabiamila.

Malami, ya yi wannan jawabin ne cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba mai taken, 'Gayyatar Buhari: NASS tana daukan matakan da suka saba wa doka'.

Majalisa bata da ikon tilasta wa Buhari ya bayyana gabanta, in ji Malami
Majalisa bata da ikon tilasta wa Buhari ya bayyana gabanta, in ji Malami. Hoto daga @Vanguardngrnews
Asali: Twitter

Majalisar ta dauki wannan matakin ne bayan halaka manoma 43 da 'yan ta'adda suka yi a garin Zabarmari na jihar Borno.

DUBA WANNAN: ASUU ta amince za ta janye yajin aiki ranar 9 ga watan Disamba, inji Ngige

An shirya cewa shugaban zai gurfana gaban majalisar a ranar Alhamis amma yanzu babu tabbacin zai amsa kirar.

A cikin sanarwar da ya fitar a ranar Laraba, Malami ya ce, "majalisar tarayya bata da iko ko karfin neman shugaban kasa ya gurfana gabanta a kan ayyukan dakarun sojoji".

Majalisar ta aike wa shugaba Muhammadu Buhari gayyatar ne don karin hare hare da ake samu na 'yan bindiga da 'yan ta'adda a kasar.

KU KARANTA: Dakatar da ni da jam'iyya ta yi ya saba doka, tsohon mataimakin shugaban APC, Eta

A wani labarin daban, kwamitin zartarwa na jam'iyyar APC mai mulki a ranar Talata ya janye sharadin takara ga wanda suka shiga ko suke shirin shiga jam'iyyar.

Sharadin zai bada damar tsayawa takara a duk wata kujerar mulki ba tare da la'akari da dadewa a jam'iyyar ba.

Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ne ya bayyana haka ga majalisa bayan kammala taron kwamitin kamar yada The Punch ta ruwaito.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel