Dillalin Paul Pogba, Mino Raiola yace ‘Dan wasansa 'bai jin dadi' zai bar Kungiyar Man Utd

Dillalin Paul Pogba, Mino Raiola yace ‘Dan wasansa 'bai jin dadi' zai bar Kungiyar Man Utd

- Akwai yiwuwar cewa Paul Pogba ba zai shekara a Manchester United ba

- Dillalin ‘dan wasan ya ce Pogba ba ya jin dadin zaman da yake yi a yanzu

- Jamie Carragher ya soki Mino Raiola, ya bada shawarar a saida Tauraron

Ta tabbata cewa ‘dan wasa Paul Pogba bai jin dadin zamansa a kungiyar Manchester United, kuma zai bar kungiyar a karshen kakar shekara mai zuwa.

Sky Sports ta ce dillalin ‘dan kwallon na kasar Faransa, Mino Raiola ya bayyana wannan a lokacin da ya yi hira da Tuttosport a cikin farkon makon nan.

Raiola ya ce tauraron ya na bukatar ‘canjin iska’, don haka ya ba kungiyar Manchester United shawarar ta rabu da ‘dan kwallon ko kuma ya tashi a bagas.

"Paul bai jin dadin Man Utd, bai iya fito wa yayi abin da ya ga dama ko abin da mutane za su so.”

KU KARANTA: Pogba ya na da COVID-19

Dillalin ya cigaba da cewa: “Yana bukatar ya canza kungiya, ya na bukatar ‘canjin-iska. Ya sa hannu a kwantiragin da zai kare a kakar shekarar 2022...”

Raiola ya ce: “Amma abin da yafi wa kowa shi ne a rabu a kakar shekara mai zuwa.” Idan aka jira sai nan da shekara daya da rabi, za a samu Pogba kyauta.

Kafin yanzu kocin Manchester, Ole Gunnar Solskjaer ya nanata cewa Pogba ba zai je ko ina ba.

Amma tsohon ‘dan wasan Liverpool, Jamie Carragher ya yi kaca-kaca da dillalin ‘dan wasan mai shekara 27, sannan ya ba Manchester shawara ta saida shi.

KU KARANTA: Pogba ya yi magana game da addinin musulunci

Dillalin Paul Pogba, Mino Raiola yace ‘Dan wasansa 'bai jin dadi' zai bar Kungiyar Man Utd
Paul Pogba da Kocin Kungiyar Man Utd Hoto: manchestereveningnews.co.uk
Asali: UGC

Jamie Carragher ya na ganin ana zuzuta Pogba wanda ya ci kwallo daga dawowarsa daga jinya.

Kwanaki kun ji ana ta rade-radin Paul Pogba ba zai kara bugawa kasarsa kwallo ba saboda kalaman da shugaban Faransa ya yi a kan addinin Islama.

Daga baya ‘Dan wasan mai shekara 27 wanda ya buga wa Faransa wasanni 72 ya musanya maganar, ya yi barazanar shiga kotu da masu yada jita-jitar.

Tsohon 'dan wasan Juventus, Pogba, ya na ganin wasu gidajen jaridu ba su yin abin da ya dace wajen buga labarai, tauraron ya bayyana haka ne a Twitter.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel