Gwamnonin Najeriya 36 zasu gana da Buhari kan lamari saro

Gwamnonin Najeriya 36 zasu gana da Buhari kan lamari saro

Gwamnonin Najeriya 36 sun yanke shawaran ganawa da shugaba Muhammadu Buhari na ba da dadewa ba domin tattauna lamarin tsaro a fadin tarayya, musamman bisa abin da ya faru a Borno.

Gwamnonin sun yanke hakan a zaman kungiyar gwamnonin Najeriya NGF a ranar Laraba, The Nation ta ruwaito.

Gwamnonin da kungiyar ta aike jihar Borno domin jajantawa gwamna Babagana Umara Zulum ranar 1 ga Disamba sun dawo musu da bayanan abinda suka ganewa idanuwansu a Garin Kwashebe a karamar hukumar Jere ta jihar.

A takardar da kungiyar gwamnonin NGF ta saki a Abuja ranar Juma'a, sun ce zasu goyi bayan duk wani abu da za'ayi domin gyara hukumar yan sanda.

Karin bayani na nan tafe....

Gwamnonin Najeriya 36 zasu gana da Buhari kan lamari saro
Gwamnonin Najeriya 36 zasu gana da Buhari kan lamari saro
Asali: UGC

Asali: Legit.ng

Online view pixel