Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje

Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje

- Hussaini Mairiga, shugaban tsagin jam'iyyar APC a jihar Kano, ya sanar da sauke daya tsagin da ke karkashin jagorancin Abdullahi Abbas

- Mairiga ya ce Abbas da sauran mukarrabana sun samu shugabanci ne ta barauniyar hanya

- Kazalika, ya gargadi ma su burin shiga takarar zaben kananan hukumomi su guji siyen fom din takara daga wurin shugabancin Abbas

Wani tsagin jam'iyyar APC a jihar Kano, a karkashin jagorancin Hussaini Isa Mairiga, ya sanar da sauke shugabannin tsagin jam'iyyar a karkashin jagorancin Abdullahi Abbas, kamar yadda Thecable ta rawaito.

An sake zaben shugabannin tsagin jam'iyyar APC da ke karkashin jagorancin Abbas a shekarar 2018 saboda rikicin da ya dabaibaye jam'iyyar a shekarar 2017.

Tsagin da Abbas ya ke jagoranta shine mai daurin gindin gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar ganduje.

Da ya ke magana da manema labarai a ranar Alhamis, Mairiga ya ce Abbas da sauran mukarabbansa sun karbi shugabancin APC ne ta barauniyar hanya, ta hanyar zaben da ya raba kan mambobin jam'iyya.

KARANTA: Jami'ar kasar Amurka ta dauki Ganduje aikin lakcarin a matakin Farfesa

"Ta hanyar zaben bogi Abdullahi Abbas ya zama shugaban jam'iyya, amma duk da hakan, ya gaza tabuka komai bayan mulkin kama karya.

Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje
Siyasar Kano: APC ta sauke shugabannin jam'iyyar ma su biyayya ga Ganduje @Solacebase
Asali: Twitter

"Ba halastattun shugabanni bane, shugabancinsu ya sabawa kundin tsarin mulkin jam'iyya, a saboda haka duk wani abu da ya fito ta karkashinsu haramtacce ne.

"Abinda na ke nufi a nan shine; duk wani dan takarar a zaben kananan hukumomi da za'a yi a watan Janairu kar ya sayi fom din takara ta hannun haramtattun shugabanni.

KARANTA: Hotunan baturen dan sanda a Najeriya sun haifar da cece-kuce

"Duk Wanda ya shiga takara ta hannunsu ya shiga asara don ko ya ci zabe sai an kwace a kotu," a cewarsa.

A karshe Mairiga ya bukaci shugabancin APC na kasa ya kafa kwamitin riko na jam'iyyar a jihar Kano domin ya gudanar da sabon zaben shugabanni na gaskiya.

Legit.ng Hausa ta walafa rahoton cewa jam'iyyar PDP mai hamayyya ta rabu gida biyu a jihar Kano a yayin da zaben kananan hukumomi ke karatowa.

Hukumar zabe ta jihar Kano (KANSIEC) ta tsayar da ranar 16 ga watan Janairu a matsayin ranar zaben kananan hukumomi

A ranar Talata, 2 ga watan Disamba, tsagin Kwankwasiyya na jam'iyyar PDP a Kano ya sanar da cewa ba za su shiga a fafata da su a zaben ba.

Don sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel