Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ya gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9

Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ya gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9

- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ba dan majalisar wakilai, Umar Sani Dan Galadima wa’adin kwanaki tara ya gabatar da Faisal Maina a gabanta

- Dan majalisar mai wakiltan mazabar Kaura Namoda na jihar Zamfara dai shine ya tsaya har aka bayar da belin wanda ake karan

- Justis Okon Abang ya ce idan har hakan bai samu ba toh Dan Galadima zai biya naira miliyan 60 da ke yarjejeniyar bayar da belin ko kuma a tura shi gidan maza

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta ba dan majalisar wakilai mai wakiltan mazabar Kaura Namoda na jihar Zamfara, Umar Sani Dan Galadima zuwa ranar 4 ga watan Disamba, ya gabatar da Faisal, dan Abdulrasheed Maina wanda ya gudu bayan beli.

An gurfanar da Faisal a gaban kotu kan laifukan da suka shafi zambar kudade.

An bayar da belinsa a watan Disamban 2019, inda Dan Galadima ya tsaya masa a matsayin jingina bayan ya sanya hannu a yarjejeniyar naira miliyan 60, The Nation ta ruwaito.

Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ta gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9
Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ta gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9 Hoto: RautersNG.com
Asali: Twitter

KU KARANTA KUMA: Lauya ya yi watsi da Abdulrasheed Maina, yana neman janyewa daga shari’arsa

Justis Okon Abang, da yake zartar da hukunci a ranar Laraba, 25 ga watan Nuwamba, ya umurci Dan Galadima, wanda ya halarci zaman kotun, da ya gabatar da Faisal a ranar 4 ga watan Disamba.

Ko a kwace masa naira miliyan 60 da yayi alkawari a yayinda yake karban belin Faisal, ko kuma a tura shi gidan yari har sai ya gabatar da wanda ake kara.

A wani labarin, babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Alhamis, 26 ga watan Nuwamba, za ta saurari bukatar neman bayar da belin sanata mai wakiltan Borno ta Kudu, Ali Ndume.

An tsare Ndume a gidan yari tun ranar Litinin, kan tsayawa tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina, da yayi, inda shi kuma ya tsere.

KU KARANTA KUMA: Ka fito da kanka don kare Ndume daga wannan tozarcin, dan uwan Maina ya roke shi

Maina na fuskantar tuhume-tuhume na zambar kudade har naira biliyan biyu kafin aka bayar da belinsa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel