Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ya gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9

Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ya gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9

- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ba dan majalisar wakilai, Umar Sani Dan Galadima wa’adin kwanaki tara ya gabatar da Faisal Maina a gabanta

- Dan majalisar mai wakiltan mazabar Kaura Namoda na jihar Zamfara dai shine ya tsaya har aka bayar da belin wanda ake karan

- Justis Okon Abang ya ce idan har hakan bai samu ba toh Dan Galadima zai biya naira miliyan 60 da ke yarjejeniyar bayar da belin ko kuma a tura shi gidan maza

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta ba dan majalisar wakilai mai wakiltan mazabar Kaura Namoda na jihar Zamfara, Umar Sani Dan Galadima zuwa ranar 4 ga watan Disamba, ya gabatar da Faisal, dan Abdulrasheed Maina wanda ya gudu bayan beli.

An gurfanar da Faisal a gaban kotu kan laifukan da suka shafi zambar kudade.

An bayar da belinsa a watan Disamban 2019, inda Dan Galadima ya tsaya masa a matsayin jingina bayan ya sanya hannu a yarjejeniyar naira miliyan 60, The Nation ta ruwaito.

Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ta gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9
Wata sabuwa: Kotu ta umurci ɗan majalisar tarayya ta gurfanar da ɗan Maina nan da kwanaki 9 Hoto: RautersNG.com
Asali: Twitter

KU KARANTA KUMA: Lauya ya yi watsi da Abdulrasheed Maina, yana neman janyewa daga shari’arsa

Justis Okon Abang, da yake zartar da hukunci a ranar Laraba, 25 ga watan Nuwamba, ya umurci Dan Galadima, wanda ya halarci zaman kotun, da ya gabatar da Faisal a ranar 4 ga watan Disamba.

Ko a kwace masa naira miliyan 60 da yayi alkawari a yayinda yake karban belin Faisal, ko kuma a tura shi gidan yari har sai ya gabatar da wanda ake kara.

A wani labarin, babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Alhamis, 26 ga watan Nuwamba, za ta saurari bukatar neman bayar da belin sanata mai wakiltan Borno ta Kudu, Ali Ndume.

An tsare Ndume a gidan yari tun ranar Litinin, kan tsayawa tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina, da yayi, inda shi kuma ya tsere.

KU KARANTA KUMA: Ka fito da kanka don kare Ndume daga wannan tozarcin, dan uwan Maina ya roke shi

Maina na fuskantar tuhume-tuhume na zambar kudade har naira biliyan biyu kafin aka bayar da belinsa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng