Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis

Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis

- Za a fara sauraron bukatar neman belin Sanata Ali Ndume mai wakiltan yankin Borno ta Kudu

- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta saka ranar Alhamis, 26 ga watan Nuwamba domin fara zama

- An dai tsare Ndume ne bayan ya gaza gabatar da tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina wanda ya tsayawa a matsayin jingina

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Alhamis, 26 ga watan Nuwamba, za ta saurari bukatar neman bayar da belin sanata mai wakiltan Borno ta Kudu, Ali Ndume.

An tsare Ndume a gidan yari tun ranar Litinin, kan tsayawa tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina, da yayi, inda shi kuma ya tsere.

Maina na fuskantar tuhume-tuhume na zambar kudade har naira biliyan biyu kafin aka bayar da belinsa.

Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis
Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

A ranar 18 ga watan Nuwamban 2020, Justis Okon Abang, ya soke belin da aka baiwa Maina, yayi umurnin kama shi sannan ya bayar da izinin ci gaba da shari’arsa a bayan idonsa.

KU KARANTA KUMA: Mutumin da matarsa ta haifi yan uku ya koka, ya roki yan Najeriya su kawo masa tallafi

Alkalin a ranar Litinin, ya kuma tsare Ndume a gidan yari har sai ya gabatar da Maina ko kuma ya biya kudi naira miliyan 500 don belinsa a asusun tarayya.

Alkalin, a yayin ci gaba da zama a bayan idon Maina, a ranar Laraba, ya sa hannu a takardar neman beli da lauyan Ndume ya cike, jaridar The Nation ta ruwaito.

Ya ce an janyo hankalinsa ga bukatar neman belin da misalin karfe 8:58am na ranar Laraba, inda ya bayyana cewa a nan take ya yi umurnin fara sauraron lamarin a ranar Alhamis.

Ya kuma bayyana cewa ya yi umurnin mika takardar lokacin sauraron karar ga bangarorin da abun ya shafa.

KU KARANTA KUMA: Tsaida sunnah: Kebbi ce jihar da ta fi kowacce yawan maza masu auren mata 2 a Nigeria

Koda dai lauyan Ndume baya a kotu, lauyan EFFF, Mohammed Abubakar, ya tabbatar da cewa ya samu takardar fara sauraron lamarin.

A gefe guda, dan uwan tsohon Shugaban hukumar ta fansho, Aliyu Maina ya bukaci kawun nasa a kan ya gabatar da kansa ga rundunar yan sanda.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Aliyu ya ce sake bayyanar Maina zai dakatar da tozarcin da Ndume ke fuskanta a idon duniya kafin lamarin ya tabarbare.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng