Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis

Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis

- Za a fara sauraron bukatar neman belin Sanata Ali Ndume mai wakiltan yankin Borno ta Kudu

- Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta saka ranar Alhamis, 26 ga watan Nuwamba domin fara zama

- An dai tsare Ndume ne bayan ya gaza gabatar da tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina wanda ya tsayawa a matsayin jingina

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Alhamis, 26 ga watan Nuwamba, za ta saurari bukatar neman bayar da belin sanata mai wakiltan Borno ta Kudu, Ali Ndume.

An tsare Ndume a gidan yari tun ranar Litinin, kan tsayawa tsohon shugaban hukumar fansho, Abdulrasheed Maina, da yayi, inda shi kuma ya tsere.

Maina na fuskantar tuhume-tuhume na zambar kudade har naira biliyan biyu kafin aka bayar da belinsa.

Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis
Yanzu Yanzu: Za a fara sauraron bukatar bayar da belin Ndume a ranar Alhamis Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

A ranar 18 ga watan Nuwamban 2020, Justis Okon Abang, ya soke belin da aka baiwa Maina, yayi umurnin kama shi sannan ya bayar da izinin ci gaba da shari’arsa a bayan idonsa.

KU KARANTA KUMA: Mutumin da matarsa ta haifi yan uku ya koka, ya roki yan Najeriya su kawo masa tallafi

Alkalin a ranar Litinin, ya kuma tsare Ndume a gidan yari har sai ya gabatar da Maina ko kuma ya biya kudi naira miliyan 500 don belinsa a asusun tarayya.

Alkalin, a yayin ci gaba da zama a bayan idon Maina, a ranar Laraba, ya sa hannu a takardar neman beli da lauyan Ndume ya cike, jaridar The Nation ta ruwaito.

Ya ce an janyo hankalinsa ga bukatar neman belin da misalin karfe 8:58am na ranar Laraba, inda ya bayyana cewa a nan take ya yi umurnin fara sauraron lamarin a ranar Alhamis.

Ya kuma bayyana cewa ya yi umurnin mika takardar lokacin sauraron karar ga bangarorin da abun ya shafa.

KU KARANTA KUMA: Tsaida sunnah: Kebbi ce jihar da ta fi kowacce yawan maza masu auren mata 2 a Nigeria

Koda dai lauyan Ndume baya a kotu, lauyan EFFF, Mohammed Abubakar, ya tabbatar da cewa ya samu takardar fara sauraron lamarin.

A gefe guda, dan uwan tsohon Shugaban hukumar ta fansho, Aliyu Maina ya bukaci kawun nasa a kan ya gabatar da kansa ga rundunar yan sanda.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Aliyu ya ce sake bayyanar Maina zai dakatar da tozarcin da Ndume ke fuskanta a idon duniya kafin lamarin ya tabarbare.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel