Jerin lokutan da Buhari ya tafi jinya Ingila tsakanin 2015 da yanzu

Jerin lokutan da Buhari ya tafi jinya Ingila tsakanin 2015 da yanzu

Tun lokacin da ya hau mulki a 29 ga Mayun 2015, shugaba Buhari ya tafi jinya wata biyar,kuma ya kwashe kwanaki 170 cikin kwanaki 1,987 na mulkinsa a Landan.

Legit ta kawo muku cewa, a ranar Alhamis ne majalisar dattijai ta gargadi ma'aikatan fadar shugaban kasa (Asorock Villa) su dakatar da shugaba Buhari daga fita waje domin a duba lafiyarsa.

A cewar majalisar, yin hakan zai tabbatar da cewa asibitin fadar shugaban kasa ya koma hayyacinsa a cikin shekarar nan.

Kwamitin majalisar dattijai a kan tabbatar da daidaito da alaka a tsakanin bangarorin gwamnati ne ya yi wannan gargadi yayin da babban sakataren fadar shugaban kasa, Tijjani Umar, ya bayyana a gabansa domin kare kasafi kudin shekarar 2021.

Karanta cikakken labarin a nan

Jerin lokutan da Buhari ya tafi jinya Ingila tsakanin 2015 da yanzu
Jerin lokutan da Buhari ya tafi jinya Ingila tsakanin 2015 da yanzu
Asali: UGC

KAI TSAYE: Sakamakon zaben kasar Amurka sun fara fitowa, Trump 214, Biden 264

Jaridar Vanguard ta tattaro lokutan da shugaban kasa ya tafi jinya kasar waje.

Ga jerin nan mun kaow muku:

- Febrairu 5-10, 2016: Buhari ya dau hutun kwanaki shida zuwa Birtaniya inda yayi ikirarin cewa Likitocinsa na zaune a Ingila.

- 6-19 ga Yuni, 2016: Buhari ya tafi jinyar ciwon kunne Ingila inda ya kwashe kwanaki 13.

- 19 ga Junairu, 2017: Buhari ya kara zuwa Landan hutun jinya

- 5 ga Febrairu, 2017: Buhari ya aika wasika majalisar dokoki inda ya bukaci tsawaita kwanakin zamansa a Landan

Sai ranar 10 ga Maris, 2017 shugaban kasan ya dawo Najeriya amma bai koma bakin aiki ba. Hadimansa

- 7 ga Mayu, 2017: Buhari ya sake komawa Landan jinya. Bai dawo ba sai da ya kwashe kwanaki 104.

- 19 ga Agusta, 2017: Buhari ya dawo Najeriya, amma bai koma ofis ba saboda beraye sun bata ofishinsa, cewar fadar shugaban kasa.

- 8 ga Mayu, 2018: Buhari ya sake zuwa Landan duba lafiya

KU KARANTA: EndSARS: Akwai bukatar Sarakuna su ba gwamnati goyon-baya inji Buhari

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng