Za a samu hauhawar wadanda zasu kamu da cutar korona a karo na biyu - FG

Za a samu hauhawar wadanda zasu kamu da cutar korona a karo na biyu - FG

- Yawan masu korona a Najeriya zai karu sosai nan da makonni biyu masu zuwa

- Babban sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha ne ya tabbatar da hakan a ranar Talata, 3 ga watan Nuwamba

- Mustapha ya ci gaba da bayyana cewa zabukan gwamnan Edo da Ondo, da kuma zanga-zangar EndSARS ne za su haddasa haka

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da tsoron kwararru a harkar lafiya da dama a fadin duniya game da dawowar annobar cutar korona a karo na biyu.

Boss Mustapha, babban sakataren gwamnatin tarayya kuma shugaban kwamitin Shugaban kasa kan COVID-19 a ranar Talata, 3 ga watan Nuwamba, ya bayyana cewa za a fasinjoji da yawa za su shigo da cutar cikin kasar, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Mustapha ya daura laifin haka a kan wasu yan Najeriya da suka ki daukar gwaje-gwajen da ya kamata a yayinda suka iso kasar, inda ya bayyana cewa daga alkaluman mahukunta, mutum daya cikin uku ne ke gabatar da kansu don gwaji.

Za a samu hauhawar wadanda zasu kamu da cutar korona a karo na biyu - FG
Za a samu hauhawar wadanda zasu kamu da cutar korona a karo na biyu - FG Hoto: @PremiumTimesng
Asali: Twitter

KU KARANTA KUMA: Mu masu tsantsar biyayya ne ga shugaban kasa - Buratai

Babban sakataren gwamnatin ya kara da cewa zabukan Edo da Ondo, da kuma zanga-zangar EndSARS a fadin kasar, sun kara yawan cutar.

Ya ce:

“PTF na ta jaddada wadannan lamura saboda muna cikin hatsarin shigowa da cutar, tunda an bude hanyar jiragen samanmu da kuma yawan yaduwar cutar sakamakon zanga-zanga. Makonni biyu masu zuwa za su zamo cike da hatsari."

KU KARANTA KUMA: Muna kokarin hana sake barkewar zanga-zangar EndSARS a karo na biyu – Shugaban gwamnonin Arewa

Mustapha ya bayyana cewa PTF ta yi barazanar daukar mataki a kan masu take doka sannan ta lura cewa da dama basa bayar da hadin kai.

A gefe guda, mun ji cewa Gwamnatin jihar Legas na iya sa sabuwar dokar hana fita da ma wasu tsauraran matakai idan aka samu barkewar sababbin masu dauke da cutar COVID-19.

Jaridar Punch ta fitar da wannan rahoto a ranar Talata, 3 ga watan Nuwamba, 2020.

Rahoton ya ce wannan sanarwa ta fito ne daga bakin darektan yada labarai na ma’aikatar lafiyar jihar Legas, Tunbosun Ogunbanwo a ranar Talata da rana.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng