Yanzun nan: Dole ta sa an garkame Makarantu ganin zanga-zanga ta ki cinyewa

Yanzun nan: Dole ta sa an garkame Makarantu ganin zanga-zanga ta ki cinyewa

- Zanga-zangar #EndSARS da ake yi ta tursasa rufe Makarantu a Oyo

- Kafin nan gwamnonin Jihohi sun maka dokar ta-baci a Legas da Edo

- Yanzu haka Sanatoci su na zama na musamman a majalisar dattawa

Zanga-zangar da ake ta faman yi a bangarorin Najeriya ya yi dalilin da ya sa aka rufe makarantun kasuwa da na gwamnati a fadin jihar Oyo.

Wannan zanga-zanga da akasari matasa su ke gudanar wa ya jawo cikas wajen harkar karantarwa a Oyo, jim kadan da komawa karatu a kasar.

Jaridar The Nation ta ce an rufe makarantun boko a jihar duk da cewa gwamnati ba ta fitar da takarda ta na umurtar a dauki wannan mataki ba.

KU KARANTA: #IStandWithBuhari za su yi tattakin lumana a Birnin Tarayya

La’akari da yadda aka gaza kawo karshen wannan zanga-zanga bayan fiye da mako guda ya sa iyaye da dalibai su ka kaurace wa makarantu.

Makarantun kasuwa sun aika wa iyayen yara takarda a daren ranar Lahadi, su na bada shawarar a guji kawo yara makaranta saboda halin da ake ciki.

Irinsu yankin Apata, New Garage, 110, Omi Adio, Molete, Beere, Ojoo, Moniya, da titin Ibadan a jihar Oyo ba su shiguwa saboda zanga-zangar da ake yi.

A daidai wannan lokaci kuma majalisa ta kira taron gaggawa na musamman a ranar Talata.

KU KARANTA: #EndSARS Gwamnati ta sa dokar ta baci a Legas

Yanzu nan: Dole ta sa an garkame Makarantu ganin zanga-zanga ta ki cinyewa
Masu zanga-zangar EndSARS Hoto: Legit.ng
Asali: Original

Ana tunanin cewa Sanatoci sun shiga bayan labule a majalisar ne domin kawo karshen wannan zanga-zanga da ta ci bangarorin kasar daban-dabam.

Bude majalisa yau ke da wuya, Ahmad Lawan, ya bukaci ayi zaman gaggawa da karfe 10:55.

A yau aka ji cewa ‘yan zanga-zanga sun jawo aiki ya tsaya cak a Legas da karfi da yaji. Legas da ta saba tatsar kudin bin hanyoyi ta gagara yin hakan a yanzu.

Rufe manyan hanyoyi da kofofin shiga garin da aka yi ya sa jihar ta tafka asarar N230m.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel