Abun mamaki: Saurayi ya nemi auren budurwa a taron zanga zangar EndSARS, ta amince

Abun mamaki: Saurayi ya nemi auren budurwa a taron zanga zangar EndSARS, ta amince

- Wani dan Najeriya, Demola, a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, ya nemi auran masoyiyarsa a filin zanga-zangar neman a kawo karshen cin kashin da yan sanda ke yi wa jama’a

- Demola ya bayyana cewa abokansa sun kasance a wajen domin mara masa baya yayinda ya dauki wannan mataki na neman auren budurwar tasa

- Mutane da dama na ta yi wa masoyan fatan alkhairi da rayuwa mai albarka a gaba

Zanga-zangar neman a kawo karshen rundunar SARS ya dauki sabon salo a ranar Talata, 13 ga watan Oktoba, lokacin da wani matashi mai suna Demola ya nemi auran budurwarsa a wajen taron.

Idan za ku tuna dai ana gudanar da zanga-zanga a fadin kasar kan neman a soke rundunar SARS sakamakon zarginsu da ake yi da cin zarafin al’umma.

Abun mamaki: Saurayi ya nemi auren budurwa a taron zanga zangar EndSARS, ta amince
Abun mamaki: Saurayi ya nemi auren budurwa a taron zanga zangar EndSARS, ta amince Hoto: @Demo_UK
Asali: Twitter

Abunda ya ja hankali game da masoyan shine kasancewar mutane dauke da kwaleyen sanarwar baikon nasu a kewaye da wajen.

KU KARANTA KUMA: EndSARS: Babu bukatar cigaba da zanga-zanga don kun samu abinda kuke so

A kusa da masoyan, an gano wani mai zanga-zanga wanda ya kasance abokin saurayin rike da kwali da aka rubuta: “macen da ta bi ni wajen zanga-zanga za mu nema da aure.”

Matashin saurayin ya tsuguna a kan gwiwarsa yayinda ya gabatarwa da budurwar zoben alkawarin aure.

A cikin daya daga hotunan da ya wallafa a shafinsa na Twitter, an gano masoyiyar tasa tana murna da nuna zoben nata, wanda hakan ke nufin ta amince da shi a matsayin miji.

Kalli hotunansu a kasa:

KU KARANTA KUMA: Gwamnatin Nigeria za ta haramta shigo da madara daga 2022 - Ministan noma

A wani labarin kuma, 'Yan daban dake dauke da adduna sun kai wa masu zanga-zangar farmaki a daidai Berger, bayan kusan awa daya da fara zanga-zangar.

Sun ci mutuncin masu zanga-zangar har da masu wucewa, inda suka lalata ababen hawan dake wurin.

Sun lalata akalla motoci 5 take anan, sannan sun ji wa masu zanga-zangar munanan raunuka.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng