‘Yan bindiga sun sace wani jami’in hukumar kula da shige da fice da matarsa, sun kuma kashe kanwarsa a Nasarawa
Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kai farmaki gidan wani jami’in hukumar kula da shige da fice na Najeriya, Salihu Usaman, a garin Gudi da ke karamar hukumar Akwanga na jihar Nasarawa.
Sun kuma yi garkuwa da jami’in da kuma matarsa.
Wani idon shaida, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce yan bindiga sun kai mamaya gidan da misalin karfe 9:00 na daren ranar Talata.
Majiyan ya bayyana cewa ‘yan bindigan sun yi harbe-harbe domin tarwatsa matasa, wadanda suka yi kokarin dakile harin, sannan harbin ya samu mutum guda.
A cewar majiyar, ‘yan bindigan sun samu shiga gidan bayan sun tsoratar da matasan sannan suka sace jami’in da matarsa.

Source: UGC
Wani shaida ya ce, wanda aka sacen ya kasance dan uwan tsohon ministan sadarwa, Mista Labaran Maku.
Da aka tuntube shi, Kwanturolan hukumar a shige da fice a jihar, Zainab Lawal, ta tabbatar da lamarin.
KU KARANTA KUMA: Shugaban kungiyar kwadago na Najeriya reshen jihar Taraba ya rasu sakamakon cutar korona
Ta ce: “An sace jami’in NIS, Superintendent Salisu Usman da matarsa.
“An kuma harbi kanwarsa inda hakan ya yi sanadiyar mutuwarta.”
Kakakin yan sandan jihar, ASP Ramhan Nansel, bai amsa kiran waya ba a daidai lokacin kawo wannan rahoto kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
A wani labari makamancin wannan, mun ji cewa 'Yan bindiga sun sace babban limamin rundunar 'yan sandan jihar Taraba, Mallam Mustapha Nuhu.
An yi garkuwa da babban dan sandan ne a daren ranar Lahadi, 12 ga watan Yuli, jaridar Daily trust ta ruwaito.
'Yan bindigar da za su kai 10 sun tsinkayi gidan Malamin da ke kwatas din Nana Aisha a tsakar dare tare da sace shi.
Malamin kuma babban dan sandan, na aiki da rundunar 'yan sandan jihar Taraba.
An gano cewa yayi wa'azi a kan yawaitar laifuka musamman garkuwa da mutane a jihar Taraba yayin hudubar ranar Juma'a.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa, 'yan bindiga na ta kai hari a tsakiyar birnin Jalingo a cikin makonnin nan.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng