Manyan jami’an gwamnatin Benue da Taraba sun isa Nasarawa domin tattauna rashin tsaro

Manyan jami’an gwamnatin Benue da Taraba sun isa Nasarawa domin tattauna rashin tsaro

- Manyan jami’an gwamnati daga jihohin Benue da Taraba a ranar Talata, 14 ga watan Afrilu sun isa jahar Nasarawa domin ganawa kan rashin tsaro a yankin

- Mataimakin gwamnan jahar Benue, Mista Benson Abopnu da takwaransa na jahar Taraba, Alhaji Haruna Manu, ne suka jagorancin tawagarsu zuwa wajen taron

- Shugabannin siyasa, sarakunan gargajiya da kungiyoyin addini, da sauransu ma za su halarci taron ganawar, ana kuma sanya ran za a kulla yarjejeniya a karshe

Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa manyan jami’an gwamnati daga jihohin Benue da Taraba a ranar Talata, 14 ga watan Afrilu sun isa jahar Nasarawa domin ganawa kan rashin tsaro a yankin.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mataimakin gwamnan jahar Benue, Mista Benson Abopnu da takwaransa na jahar Taraba, Alhaji Haruna Manu, ne suka jagorancin tawagarsu zuwa wajen taron.

Manyan jami’an gwamnatin Benue da Taraba sun isa Nasarawa domin tattauna rashin tsaro
Manyan jami’an gwamnatin Benue da Taraba sun isa Nasarawa domin tattauna rashin tsaro
Asali: UGC

An tattaro cewa an kira taron gaggawan ne ta bangaren gwamnan jahar Nasarawa , Abdullahi Sule, domin tattauna hanyoyin magance rashin tsaro a yankin arewa ta tsakiya.

An kuma ruwaito cewa shugabannin siyasa, sarakunan gargajiya da kungiyoyin addini, da sauransu ma za su halarci taron ganawar.

Ana sanya ran kulla yarjejeniya a karshen taron.

KU KARANTA KUMA: Covid-19: Ganduje ya shiga rudani kan shawarar rufe Kano

A wani labari na daban, mun ji cewa akalla mutane 17 ne suka mutu yayin da jirgin yakin Najeriya ya jefa bamabamai a kauyen Sakotoku dake karamar hukumar Dambo ta jahar Borno, bisa kuskure.

Jaridar TheCable ta ruwaito wadanda suka mutu a wannan harin sune mata da kuma kananan yara, wanda suke wasa da zaman shan iska a karkashin wata bishiyar mangwaro.

Majiyoyi daga gidan Soja sun bayyana an jefa bamabaman ne bayan rundunar Sojan sama ta samu labarin taruwar yan Boko Haram a kauyen, don haka ta shirya musu luguden wuta.

Inda ya kamata a kai harin shi ne wani yanki a Korongilum dake makwabtaka da Sakotoku da kimanin nisan kilomita 12, a nan ne mayakan Boko Haram din suka taru.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel