An tsaurara matakan tsaro a filin jirgin sama na Oshiomhole kan zuwan Oshiomhole

An tsaurara matakan tsaro a filin jirgin sama na Oshiomhole kan zuwan Oshiomhole

- An tsaurara matakan tsaro a filin jirgin sama na Benin

- An tsaurara tsaro ne a wajen domin dakile duk wani yunkuri na ci wa Oshiomhole zarafi ko kuma hana shi barin filin jirgin

- Hakan ya biyo bayan kokawar da wasu jiga-jigan APC suka yi kan harin da ake yunkurin kai wa Oshiomhole da mukarrabansa a Abuja

- An kuma gano gugun wasu matasa jibge a filin jirgin inda suke wakokin kin jinin Oshiomhole

Rahotanni sun kawo cewa an tsaurara matakan tsaro a filin jirgin sama na Benin kan tsoron yiwuwar kunyata Shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, Kwamrad Adams Oshiomhole.

A mashigin filin jirgin saman, akwai sojoji da motocin yan sanda biyu yayinda sauran jami’an rundunar tsaro ta DSS da NSCDC suka kasance a zube a wurare daban-daban na filin jirgin.

An kuma gano motan silken a tsaro ajiye a wajen ajiye motoci na filin jirgin saman.

An tattaro cewa an tsaurara tsaro ne a wajen domin dakile duk wani yunkuri na ci wa Oshiomhole zarafi ko kuma hana shi barin filin jirgin, jaridar The Nation ta ruwaito.

An tsaurara matakan tsaro a filin jirgin sama na Oshiomhole kan zuwan Oshiomhole
An tsaurara matakan tsaro a filin jirgin sama na Oshiomhole kan zuwan Oshiomhole
Asali: UGC

Mun samu labarin cewa an gano Dr. Pius Odubu, Janar Charles Airhiavbere, Samson Osagie da sauran jiga-jigan APC masu biyayya ga Oshiomhole a filin jirgin domin tarbansa.

An kuma gano gugun wasu matasa jibge a filin jirgin. An jiyo matasan suna wakokin kin jinin Oshiomhole.

Wata majiyar tsaro ta ce wasu jiga-jigan APC sun koka kan harin da ake yunkurin kai wa Oshiomhole da mukarrabansa a Abuja.

KU KARANTA KUMA: Ladanin Masallacin Landan da aka kai wa hari da wuka yace ya yafe duniya da lahira

A watan Disamban shekarar da ya gabata, an kwantar da magoya bayan APC 15 da ke biyayya ga Gwamna Obaseki a asibiti bayan an bude masu wuta tare da sojoji da yan sanda da ke masu rakiya da kuma wasu manyan masu fada-aji ciki harda Oshiomhole a hanyarsu ta zuwa gangamin siyasa a jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng