Mu na nan a kan bakarmu na tsige Hafsun Sojoji – Majalisar Wakilai

Mu na nan a kan bakarmu na tsige Hafsun Sojoji – Majalisar Wakilai

Majalisar wakilan tarayya ta ce har yanzu ta na kan matsayar ta na cewa dole shugabannin hafsun sojojin Najeriya su yi murabus, ko kuma a tsige su.

Mai magana da yawun bakin ‘Yan majalisar wakilan kasar shi ne ya kara jaddada wannan matsaya da su ke kai a cikin karshen makon nan da ya wuce.

Honarabul Benjamin Kalu ya ke cewa Majalisar ba ta lashe amanta game da matakin da ta dauka na cewa a nada wasu sababbin hafsun sojoji a Najeriya ba.

Kalu ya fadawa ‘Yan jarida: “Ku na cikin Majalisar, kun ji wani ya tashi ya bukaci a janye wannan matsaya? Matsayarmu ta na nan, ba mu lashe amanmu ba.”

Hon. Kalu ya kara da: “Kun san aikin majalisa, kun san abin da mu ke yi, Idan har an cin ma wata matsaya, kuma ana so a canza ta, akwai hanyar da ake bi.”

KU KARANTA: 'Yan sun cafke ‘Yan Ansaru da ke da hannu wajen garkuwa da mutane

Mu na nan a kan bakarmu na tsige Hafsun Sojoji – Majalisar Wakilai
Ana kokawa da yadda ake kashe Bayin Allah dare da rana.
Asali: UGC

“Majalisa ta dauki wannan mataki. Don haka duk matsayar da mu ka cinma, ta na nan har sai ranar da wani ya bukaci a janye wannan mataki” Inji Kalu.

Kwanakin baya, Majalisar ta tsaida magana cewa a canza shugabannin sojoji domin a kawo karshen kashe-kashen da ake fama da shi a halin yanzu.

Benjamin Kalu, wanda ya ke magana a madadin ‘Yan majalisa ya ce ka da wanda ya yi tunanin sun sauko daga matsayar da su ke kai game da harkar tsaro.

Tun a shekarar 2015, shugaba Buhari ya nada hafsun soji wanda har yau bai canza su ba duk da cewa a doka, dukkaninsu sun zarce shekarun da ake yi a aiki.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewa tare da mu.

Ga masu bukatar manhajar mu na Musulunci sai a bibiyi wannan shafi

https://fb.gg/play/ramadan_ramadan

Asali: Legit.ng

Online view pixel