Shugaba Trump zai hana masu zuwa Amurka haihuwa shiga kasar

Shugaba Trump zai hana masu zuwa Amurka haihuwa shiga kasar

- Kasar Amurka ta ce daga yanzu ba za ta kara bai wa baki 'yan kasashen waje da ke zuwa haihuwa cikinta izinin shiga kasar ba

- Ma' aikatar cikin gida ta kasar ta bayyana cewa dokar za ta fara aiki ne daga ranar yau Juma'a 24 ga watan Janairu

- Daga yanzu matan da ke neman izinin shiga kasar a matsayin baki sai sun nuna wata hujja mai karfi ta son zuwa Amurkan maimakon son haihuwa a can

Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa kasar Amurka ta ce daga yanzu ba za ta kara bai wa baki 'yan kasashen waje da ke zuwa haihuwa cikinta izinin shiga kasar ba.

A wani jawabi daga ma'aikatar cikin gida ta kasar, ya bayyana cewa dokar za ta fara aiki ne daga ranar yau Juma'a 24 ga watan Janairu.

Saboda haka daga yanzu matan da ke neman izinin shiga kasar a matsayin baki sai sun nuna wata hujja mai karfi ta son zuwa Amurkan maimakon son haihuwa a can.

Mata musamman na Najeriya da dama sun mayar da Amurka wajen zuwa haihuwa domin samar wa 'ya'yansu takardun zama 'yan kasa.

KU KARANTA KUMA: Wani bawan Allah ya tsinci naira miliyan 9.7 a ATM sai ya mayar dashi cikin banki

Wannan lamari dai ya fara janyo muhawara sosai a shafukn sada zumuntar Najeriya

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng