Hafiz Idris daga jihar Borno ya lashe musabakar Al-Qur'ani ta duniya a Saudiya

Hafiz Idris daga jihar Borno ya lashe musabakar Al-Qur'ani ta duniya a Saudiya

Wani matashi dan jihar Borno, Hafiz Idris, ya shiga cikin jerin sahun 'yan Najeriya na musamman da suka yi fintinkau a fagen lashe gasar kasa-da-kasa ta duniya.

Matashin ya wakilci Najeriya a yayin gasar karatun Al'Qur'ani ta Sarki Malik Durban da aka gudanar a birnin Makkah.

Hafiz wanda ya kasance haifaffan jihar Borno a Arewa maso Gabashin Najeriya, shi ne ya fito Zakara wajen lashe musabakar karatun Al-Qur'ani ta duniya ta bana da aka gudanar a kasar Saudiya.

KARANTA KUMA: Mama Taraba ta sauya sheka zuwa jam'iyyar PDP

Ana iya tuna cewa, hazikai 13 ne daga kasashen duniya daban-daban suka samu manyan kyaututtuka na musamman a yayin gasar hadda, karatu da kuma tajwidin Al-Qur'ani karo na 40 da aka gudanar cikin birnin aminci na Madinah a bara.

Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng