Gwamna Yahaya ya nada shugaban ma'aikata da wasu sabbin hadimai hudu

Gwamna Yahaya ya nada shugaban ma'aikata da wasu sabbin hadimai hudu

A ranar Laraba ne gwamnan jihar Gombe, Alhaji Abubakar Inuwa Yahaya, ya amince da nadin Alhaji Abubakar Inuwa Kari a matsayin shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin jihar Gombe.

Kafin nada shi a sabon mukamin, Kari ya kasance darektan tsare-tsare a sakatariyar jam'iyyar APC ta kasa.

Kari ya maye gurbin Alhaji Muhammad Kabir Usman Kukan Daka, mutumin da shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya nada domin ya wakilci jihar Gombe a hukumar tsara rabon kudaden gwamnatin tarayya da aka samu daga haraji (RMAFC).

A ranar 2 ga watan Yuni ne, gwamna Yahaya ya nada Kukan Daka da wasu mutane 12 a matsayin sahun farko na mukaman da ya nada bayan rantsar da shi a matsayin zababben gwamnan jihar Gombe.

DUBA WANNAN: Tura ta kai bango: Kungiyar dattijan arewa ta umarci makiyaya su bar kudancin Najeriya

A wani jawabi da Ismaila Uba Misilli, kakakin gwamna Yahaya, ya fitar, ya bayyana cewa gwamnan ya amince da nadin wasu uku a matsayin mataimka na musamman, mutum guda daga sanatoriya uku na jihar.

Mutanen da gwamnan ya nada sune: Adamu Abdullahi Masad Biri (Gombe ta arewa), Babaiya Kombani (Gombe ta tsakiya), da Abdullahi Idris Maitama Billiri (Gombbe ta kudu).

Kazalika, gwamnan ya amince da nada Umar Chiroma Abdussalam a matsayin shugaban sashen sufuri na jihar Gombe (Gombe line)

A cewar sanarwar, dukkan sabbin nadin zasu fara aiki nan take, ba tare da bata lokaci ba.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Za ka iya aiko mana da labari ta hanyar cike wanna fom da ke kasa:

https://docs.google.com/forms/d/e/1FAIpQLSch6m8qBDJY3fmT8OH0Dy7Sqkrvwt-tveaPURetOsKjYb_4cQ/viewform

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng