Sakatarorin din-din-din da ke jagorantar ma’aikatun Najeriya a yanzu (cikakken sunayensu)
A lokacin da yake shirye-shiryen kama aiki a karo na biyu, a ranar 22 ga watan Mayu, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umurci ministoci da su mika shugabanci ga sakatarorin din-din-din na ma’aikatunsu daban-daban.
Ya kuma umurci ministocin da su mika takardun mika aikinsu ga babban sakataren gwamnatin tarayya, yayinda ya bukaci sakatarorin din-din-din da su ci gaba daga inda suka tsaya.
Shugaba Buhari ya bayar da umurnin ne a lokacin taron majalisa na karshe da suka gudanar a Abuja.
Tun bayan da suka mika aiki a tsakanin 22-28 ga watan Mayu, sakatarorin din-din-din na ma’aikatu daban-daban ne ke jagoranci.
KU KARANTA KUMA: Kalli uwargidar gwamnan jihar Gombe da ke sanya dogon hijabi har kasa
Ga jerin sunayen mukaddashin ministocin a kasa (sakatarorin din-din-din).
Ma’aikatar noma da raya karkara- Mohammed Bello
Ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsaren kasa- Ernest Umakihe
Ma’aikatar sadarwa - Istiafanus Fukur
Ma’aikatar tsaro- Nuaratu Batagarawa.
Ma’aikatar ilimi- SonnyEchono
Ma’aikatar muhalli- Odusote Abimbola
FCT- Ohaa. Chinyeaka Christain.
Ma’aikatar kudi - Mahmoud
Isa- Duste
Ma’aikatar harkokin waje - Mustapha Suleiman
Ma’aikatar lafiya - Abdullahi Abdullahi
Ma’aikatar labarai- Grace Isu Gekpe
Ma’aikatar cikin gida- Georgina Ehuriah
Ma’aikatar shari’a - Dayo Apata
Ma’aikatar kwadago da dibar ma’aikata- Williams Alo
Ma’aikatar Niger Delta- Aminu Aliyu Bisalla.
Ma’aikatar ma fetur - Yemi Esan Folasade
Ma’aikatar ayyuka da gidaje - Mohammad Bukar
Ma’aikatar wutar lantarki - Louis Edozien
ma’aikatar kimiyya da fasaha - Birtus Bako
Ma’aikatar ma’adinai - Abdulkadir Muazu
Ma’aikatar sana’o’i - Edet Sunday Akpan
Ma’aikatar sufuri - Shaibu Zakari
Ma’aikatar ruwa - Ekaro Comfort Chukwumuebobo
Ma’aikatar harkokin mata- Ifeoma Anabogwu
Ma’aikatar masa da wasanni - Olusade Adesola
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng