Wata sabuwa: Manyan hakiman fadar Sarkin Kano guda 4 sun nuna ma Ganduje yatsa

Wata sabuwa: Manyan hakiman fadar Sarkin Kano guda 4 sun nuna ma Ganduje yatsa

Manyan hakiman fadar Sarkin Kano guda hudu wadanda hakkin zaben Sarki a masarautar Kano ya rataya a wuyansu sun nuna ma Ganduje yatsa game da raba masarautar Kano, inda suka garzaya gaban kotu domin kotu ta dakatar da gwamnan.

Majiyar Legit.ng ta ruwaito manyan hakiman sun hada da Madakin Kano Yusuf Nabahani, Makaman Kano Sarki Ibrahim, Sarkin Dawaki maituta, Bello Abubakar da kuma Sarkin Bai, Mukhtar Adnan hakimin Dambatta.

KU KARANTA: Shugaban EFCC ya bayyana babban dalilin da yasa suka kaddamar da bincike akan Saraki

Wata sabuwa: Manyan hakiman fadar Sarkin Kano guda 4 sun nuna ma Ganduje yatsa
Sarkin Kano
Asali: UGC

Hakiman sun shigar da wannan kara ne gaban babbar kotun jahar Kano inda suke karar gwamna jahar Kano, kaakakin majalisar dokokin jahar, majalisar dokokin jahar, gwamnatin jahar Kano, kwamishinan shariar jahar da kuma sabbin Sarakuna masu daraja ta daya da Ganduje ya nada.

Hakiman sun nemi kotu ta haramta wannan nadi da Ganduje yayi duba da cewa sune masu ikon zaban sabon Sarki a masarautar Kano, kuma wannan nadi da yayi yayi kaca kaca da tarihin sarautar Kano, kuma ya bata musu aiki, musamman duba da cewa sune wakilan gidajen Jobawa, Sullubawa, Yolawa da Dambazawa.

Domin su nuna da gaske suke a wannan shari’ar, manyan hakiman sun dauki hayar manyan lauyoyi masu lambar SAN guda bakwai da suka hada da Lateef Fagbemi, AB Mahmoud, Adeniyi Akintola, Paul Usoro, Suraj Sa’eda, Hakeem Afolabi da Nassir Dangiri.

Wata sabuwa: Manyan hakiman fadar Sarkin Kano guda 4 sun nuna ma Ganduje yatsa
Karar
Asali: UGC

Sai kuma wasu kananan lauyoyi guda goma sha bakwai da suka hada da Maliki Kuliya, Nureini Jimoh, Nasiru Aliyu, Muritala Abdulrasheed, Aminu Gadanya, Ismail Abdulaziz, Sagir Gezawa, Rashidi Isamotu, Oseni Sefiullahi, Ibrahim Abdullahi, Haruna Zakariyya, Auwal Dabo, Badamasi Suleiman, O.O Samuel, Fariha Sani Abdullahi, Yahaya Abdulrahseed da Amira Hamisu.

Idan za’a tuna a ranar 8 ga watan Mayu ne gwamnan Kano ya kirkiri sabbin masarautu guda hudu a jahar Kano tare da nada musu sabbin Sarakuna masu daraja ta daya, masarautun da sarakunan sune kamar haka; Aminu Ado-Bayero, Bichi; Tafida Ila, Rano; Ibrahim Abdulkadir, Gaya da Ibrahim Abubakar ll, Karaye.

Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa

ko a http://twitter.com/legitcomhausa

KU LATSA: Hanyar sauko da sabuwar manhajar jaridar Legit.com Hausa cikin sauki

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com

Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel