Wankan tsarki: Matasa a Lokoja sun share, sun wanke inda Atiku yayi gangamin neman zaben sa
Wasu gungun matasa mun samu labarin cewa sun yi gangami sun yi aikin gayya wajen sharewa tare da wanke in dan takarar shugabancin kasar Najeriya a karkashin tutar jam'iyyar adawa ta PDP, Alhaji Atiku Abubakar yayi taron kamfe din sa a garin Lokoja.
Hotunan matasan dai wanda ya yadu a kafafen sadarwar zamani yana dauke ne da matasan rike da tsintsinya yayin da kuma wasu suke dauke da jarakunan ruwa suna wankewa tare da share inda jam'iyyar ta PDP da dan takarar ta suka gudanar da gangamin kamfe din su.

Asali: Facebook
KU KARANTA: Kamfanonin talla suna bijirewa tallata Atiku
Legit.ng Hausa ta tuna cewa dan takarar shugabancin kasar Najeriya a karkashin tutar jam'iyyar adawa ta PDP, Alhaji Atiku Abubakar yayi taron kamfe din sa a garin Lokoja a ranar Talatar da ta gabata.
A lokacin kamfe din, Atiku Abubakar yayi alkawarin cigaba da dukkan ayyukan gwamnatin tarayyar dake a jihar da suka hada da tashar jiragen ruwa ta Baro da kuma kamfanin mulmula karafa na Ajaokuta idan har ya lashe zaben 2019 din.
Ga dai wasu hotunan matasan nan:

Asali: Facebook

Asali: Facebook

Asali: Facebook
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng