Jerin Gwanayen Takara na jam'iyyar PDP da APC da aka tsayar a jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Benuwe, Filato
A yayin da guguwar siyasa tayi kane-kane a fadin jihohin kasar nan ta Najeriya, an gudanar da zaben fidda gwanayen takarar kujerun gwammna na jam'iyyu daban-daban inda tuni sakamakon zabenya bayyana kamar yadda shafin jaridar The Punch ya ruwaito.
Binciken manema labarai ya tabbatar da cewa, an gudanar da zaben fidda gwanayen takarar kujerun gwamna na jihohi daban-daban, inda a yau Legit.ng ta kawo mu ku sakamakon zaben na jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Benuwe da kuma Filato.
Ga yadda sakamakon zaben ya kasance da aka gudanar a karshen mako kamar haka:
Jihar Filato
Laftanar Janar Jeremiah Useni mai ritaya - PDP
Simon Lalong - APC
Jihar Adamawa
Umar Fintiri - PDP
An dage zaben fidda gwani na jam'iyyar a sakamakon dambarwar siyasa da ta mamaye jihar Adamawa.
Jihar Kaduna
Isa Ashiru - PDP
Gwamna Nasir El-Rufa'i - APC
KARANTA KUMA: Rikici ya haɗiɗiye Zaben fidda Gwani na jihohin Neja, Taraba, Imo da Bauchi
Jihar Benuwe
Gwamna Samuel Ortom - PDP
Emmanuel Jime - APC
Jihar Nasarawa
Mista David Umbugadu - PDP
Mista Abdullahi Aude-Sule - APC
Na nan tafe: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mu na ci gaba da godiya a yayin kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Domin shawara ko bamu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:
https://business.facebook.com/pg/naijcomhausa
https://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng