Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari

Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari

Uwargidan shugaban kasar Najeriya, Hajiya Aisha Muhammadu Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya ga iyayen matukin jirgin Sojin Saman Najeriya, Baba-Ari da ya rasu sakamakon hatsarin jirgin da ya yi a ranar Lahadi, 30 ga watan Satumba a Katampe, Abuja.

Jirgin Baba-Ari ya yi karo ne da wani jirgin na Sojin Saman Najeriya a yayin da suke shirye-shiryen bukukuwar zagoyowar samun 'yancin Najeriya a babban birnin tarayya Abuja.

Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: PDP ta bani cin hancin makudan miliyoyi don na bar APC - Sanatar Arewa

Shugaban hafsoshin Sojin Saman Najeriya, AVM Abubakar Saddiq tare da wasu jiga-jigan Sojojin Najeriya da masu fada a ji duk sun hallarci jana'izar marigayi Baba-Ari wanda ya rasu sa'o'i kadan bayan afkuwar hatsarin.

Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Asali: Twitter

Sauran matukan jirgin da hatsarin ya ritsa dasu suna asibiti inda suke samun kulawar likitoci.

Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Asali: Twitter

Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Aisha Buhari ta kai ziyarar ta'aziyya gidansu Baba-Ari
Asali: Twitter

A wata rahoton, Legit.ng ta kawo muku cewa wani dan takarar gwamna a karkashin jam'iyyar Labour Party na jihar Kwara, Issa Arewa ya shawarci shugaba Muhammadu Buhari ya karrama marigayi Baba-Ari da lambar yabo na kasa saboda ya sadaukar da rayuwansa ne wajen yiwa kasarsa hidima.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164