Wata mace Kirista ta zama gwamna a kasar Misra a karon farko

Wata mace Kirista ta zama gwamna a kasar Misra a karon farko

Shugaba Abdel-Fattah al-Sissi na kasar Masar ya rantsar da sabbin gwamnoni 12 cikinsu har da gwamna mace na farko a jihar wadda ta fito daga mabiya addinin kirista marasa rinjaye a jihar.

An rantsar da Manal Mikhail a matsayin gwamnan jihar Damietta, wannan na nuna Mikhail ta kafa tarihi a matsayin mace Kirista ta farko da ta fara rike wannan matsayin kamar yadda al-Masry al-Youm ta ruwaito.

Kafin a nada ta gwamna, macen mai shekaru 51 ta rike mukamin mataimakiyar gwamna a Giza, garin da husumiyar Masar suke.

Mace Kirista ta karbi ragamar mulkin yanki a Misra kasar Islama
Mace Kirista ta karbi ragamar mulkin yanki a Misra kasar Islama
Asali: Twitter

Kasar Masar ce ke da adadin mabiya addinin Kirista mafi yawa a cikin kasashen gabas ta tsakiya. Adadin mabiya addinin Kirista a Masar ya kai 10% cikin adadin mutane 95 miliyan da ke kasar.

DUBA WANNAN: A karo na farko bayan tsige shi, Lawal Daura ya yi magana kan mamaye majalisa

Mabiya addinin kirista a Masar sun dade suna kokawa kan wariya da matsin lamba da musulmi ke musu a kasar.

Al - Sissi duk da cewa musulmi ne yana da farin jini a wajen mabiya addinin Kirista a kasar. Ya goyi bayan hambarar da tsohon shugaban kasar Mohammed Morsi bayan jama'a sunyi zanga-zanga bisa salon mulkinsa na raba kan jama'a.

Al-Sissi yana kusantar mabiya addinin Kirista a kasar musamman idan akayi la'akari da cewa ya kai ziyara da dama zuwa babban Cocin kasar da ke Cairo duk bayan hawansa mulki a shekarar 2014.

A shekarar 2016, magoya bayan al-Sissi sun amince da kudirin dokar sassauta dokokin neman izinin gina Coci a kasar wanda aka dade ana neman majalisar ta amince da shi.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164