Sai dai wani ikon Allah ne kadai zai sa Ganduje na APC ya yi nasara a Kano – Tsohon mataimakin gwamna

Sai dai wani ikon Allah ne kadai zai sa Ganduje na APC ya yi nasara a Kano – Tsohon mataimakin gwamna

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Hafiz Abubakar ya bayyana cewa da wuya idan gwamnan jihar Kano, Abdulahi Ganduje zai zake lashe zabe a 2019.

Tsohon gwamnan wanda yayi murabus daga matsayinsa kuma ya sauya sheka daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) yayi bayanin cewa ya bar matsayinsa ne saboda banbacin ra’ayi da aka kasa sasantawaa tsakaninsa da gwamnan jihar Kano.

Sai dai wani ikon Allah ne kadai zai sa Ganduje na APC ya yi nasara a Kano – Tsohon mataimakin gwamna
Sai dai wani ikon Allah ne kadai zai sa Ganduje na APC ya yi nasara a Kano – Tsohon mataimakin gwamna

Abubakar yace wani ikon Allah ne kadai zai iya sa jam’iyya mai mulki tayi nasara a jihar saboda tsagun dake bangon APC, jaridar Punch ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: An kama wani Mahauci da ya kware wurin yanka Kare yana gasawa ya sayarma da mutane

A wani lamari na daban, kungiyar yakin neman zaben Buhari (BCO) a daren ranar Lahadi, 12 ga watan Agusta ta sha alwashin kai mamaya majalisar dokokin kasar idan har shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki bai yi murabus daga ofis ba.

Shugaban kungiyar, Danladi Fasali ya bayyana shirin kungiyar yayinda yake Magana a lokacin kaddamar da sakatariyar kungiyar magoya bayan Buhari na jihar Ogun.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel