Hajiya Aisha Buhari tana wakiltan Najeriya a kasar Itopiya (Hotuna)
Uwargidan shugaban kasan Najeriya, Hajiya Aisha Muhammadu Buhari, ta tafi kasar Itopiya domin wakiltan Najeriya a taron OAFLA da ke gudana yanzu a Addis Ababa, babban birnin kasar Itopiya.
Aisha Buhari na halartan taron tare da dukkan sauran matan shugabannin kasashen Afrika da kewaye.
![Hajiya Aisha Buhari tana wakiltan Najeriya a kasar Itopiya (Hotuna) Hajiya Aisha Buhari tana wakiltan Najeriya a kasar Itopiya (Hotuna)](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt2g0ran8iqd4g.jpeg?v=1)
Hajiya Aisha ta tafi kasar Landan kwanakin baya domin ganawa da maigidanta wanda ke jinya a Landan, amma wasu rahtotanni sun bayyana daga baya cewa bata samu daman ganawa da shi.
![Hajiya Aisha Buhari tana wakiltan Najeriya a kasar Itopiya (Hotuna) Hajiya Aisha Buhari tana wakiltan Najeriya a kasar Itopiya (Hotuna)](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt5edgt43a3dp.jpeg?v=1)
Kana kwamred Shehu Sani yayi kira ga sanatocin da ke kokarin tilasta shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, nada kwamitin binciken cikin al’amarin rashin lafiya Buhari.
KU KARANTA: Yakubu Gowon ya bayyana mafita a Najeriya
Yace a maimakon haka kawai su hada karfi da karfe wajen taimaka masa da addu’a.
https://www.facebook.com/naijcomhausa/#
https://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng