Jihar Rivers
Babbar kotun jihar Ribas mai zama a Fatakwal ta rusa kwmaitin rikon kwarya na jam'iyyar APC a jihar Ribas, ta ce an yi kuskure wajen korarar zababbun shugabanni.
Wani abin fashewa da ake kyautata zaton bam ne ya tarwatsa sakatariyar jam'iyyar APP da ke yankin Fatakwal a jihar Ribas da tsakar daren wayewar Litinin.
Wasu 'yan daba a jihar Rivers sun yi yunkurin kawo cikas kan zanga-zangar da ake yi a kan tsadar rayuwa a kasar nan. Sun bugi wasu masu zanga-zanga.
Jam'iyyar APC a jihar Rivers ta shiga damuwa bayan yan daba da suka kona mata sakatariya sun mata barazanar cewa za su dawo. Ta nemi agaji wajen yan sanda.
Matasa masu zanga zangar adawa da tsadar rayuwa sun kewaye gidan ministan Abuja, Nyesom Wike a birnin Fatakwal da ke jihar Rivers suna ihu da taken Najeriya.
Wasu tsagerun ƴan daba da suka saje da masu zanga zanga sun tafka ɓarna a hedkwatar jam'iyyar APC da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribas, sun lalata kayayyaki.
Zanga-zanga a Najeriya ta sauya sabon salo bayan matasa sun tare tawagar motocin Gwama Siminalayi Fubara na jihar Rivers inda suka bukaci ya fito ya musu jawabi.
Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya bayyana cewa duk wanda yake sha'awar fita zanga-zanga ga fili nan ga mai doki, su kam za su zauna su ci abinci.
Tsofaffin shugabannin ƙananan hukumomi 23 da aka sallama sun yi barazana ga Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Rivers kan kin bin umarnin Kotun Koli.
Jihar Rivers
Samu kari