Jami'o'in Najeriya
A baya-bayan nan ne wani jerin sunaye da aka ce farfesoshin boge ne a jami'o'in Najeriya ya fito, sai dai jami'o'i da dama sun fito sun nesanta kansu daga sunayen.
Gwamna Agbu Kefas ya ce nan gaba kadan za a dakatar da daukar masu kwalin NCE aikin koyarwa a jihar Taraba, sai kana da kwalin digiri na daya ko na biyu.
Umar Audu, dan jarida mai bincike ta karkashin kasa ya roki gwamnatin Najeriya ta tabbatar da bashi tsaro biyo bayan rahotonsa na jami'o'i masu bada digirin bogi.
Shugaban kungiyar NANS reshen jami'o'in Benin, Ugochukwu Favour ya nemi a kama dan jaridan da ya yi rahoton 'digiri dan Kwatano', inda ya ce barazana ne ga gwamnati.
Akwai dalibai 15, 000 da suke karatu a jami’o’in da aka tsaida karbar takardar shaidarsu a Benin. Kungiyar NANS ta roki gwamnatin Najeriya ta guji yin kudin goro.
Gwamnatin tarayya ta na kukan rashin kudi, ana shirin hada ta da aiki. Ana so a kafa sababbin jami’o’i 47, da FCE 32 da manyan asibitoci 56 a jihohi
Hukumar kula da jami’o’i ta kasa (NUC), ta bayyana cewa ta kama wasu mutane da laifin gudanar da ayyukan haramtattun jami’o’i 37 a fadin kasar nan.
Gwamnatin tarayya za ta kara tsawaita dakatar da karbar digiri daga kasashen Kenya, Uganda da Nijar bayan an gano yadda ake samun digirii na bogi.
Rahotanni sun yi ta yawo kan dan jaridar da ya bankado yadda ake samun digirin bogi daga wata jami'a a Jamhuriyar Benin. Dan jaridar ya ce N600k kawai ya kashe.
Jami'o'in Najeriya
Samu kari