Zaben jihohi
Shugaba Tinubu da gwamnoni sun bukaci 'yan Najeriya da su rundumi soyayya, zaman lafiya, da hadin kai yayin bikin Kirsimeti. Diri ya nemi a taimaki marasa galihu.
Popoola Olukayode Joshua, tsohon dan takarar gwamna na NNPP a Oyo, na shirin komawa APC. Ganduje ya bukaci shiri tun wuri don tazarcen Tinubu da nasarar APC a 2027.
Kwanaki shida bayan shugaban APC, Abdullahi Ganduje ya sha alwashin kwace jihar Rivers, an roke shi ya yi kokarin karbe ikon Oyo daga jam'iyyar PDP.
APC ta fara zage damtse kafin zaben 2027. Jam'iyyar ta rasa Adamawa a zaben 2023. Ankafa kwamitin mutum takwas domin daidaita 'yan jam'iyyar kafin zaben.
Tsohon ministan kwadago a lokacin gwamnatin Muhammadu Buhari, Chris Ngige, ya ce shugabannin kananan hukumomi sun fi wasu gwamnonin karbar cin hanci da rashawa.
Wata kungiyar matasa 'yan asalin Legas sun bukaci Seyi, dan Shugaba Bola Tinubu da ya cire tunanin zaman gwamnan jihar Legas a 2027 domin ba za su bari ba.
A wannan rahoton, za ku ji cewa gamayyar kungiyar matasa ta Coalition of Nigerian Youth Leaders (CONYL) ta fadi wanda ta ke so ya zama gwamnan Legas.
An kammala zaben Ondo kuma APC ta yi nasara a 2024. Ganduje, Obasanjo na cikin waɗanda suka samu nasara. PDP, Umar Damagun na cikin waɗanda suka yi asara.
Rahoton Yiaga Africa ya nuna yadda APC da PDP saka saye kuri'u a zaɓen Ondo. Talakawa sun sayar da kuri'unsu a zaben a kan N5,000 zuwa N10,000 a zaben Ondo.
Zaben jihohi
Samu kari