Kotun Kostamare
Mallam Sani Umar, mahaifin yarinyar da aka yi wa kisan gilla a Kano ya roki Abba Kabir da ya dakatar da sauya wurin shari'ar saboda komai na iya faruwa.
An gurfanar da matar ne mai suna Hafsa bisa zargin ta yi wa mijinta dukan tsiya kan hira da 'yan mata a waya. Kotu ta kulle ta zuwa 11 ga watan Disamba, 2023.
Babbar kotun jihar Kano ta sanya ranar 6 ga watan Disamba na wannan shekara a matsayin ranar yanke hukunci kan shari'ar dan China saboda kisan budurwarsa, Ummita.
Kungiyar fafutukar tabbatar da adalci da shugabanci na gari (AJGG) ta yi kira ga hukunta Haruna Isa Dederi, Atoni Janar kuma kwamishinan shari’a na jihar Kano.
Kotun Daukaka Kara da ke zamanta a Abuja ta kori ‘yan majalisar wakilai akalla goma sha daya daga jam’iyyar PDP a ranar Juma’a 24 ga watan Nuwamba.
Femi Falana, babban lauyan Najeriya, ya ce sabanin tunanin jama’a, kotun daukaka kara reshen Abuja, ba ta soke zaben gwamna Yusuf na jihar Kano ba.
Jam’iyyar APC ta yi ikirarin cewa sabon kwafin takardar CTC na hukuncin kotun daukaka kara kan shari'ar Kano kuskure ne na rubutu da kotu za ta gyara.
Magidancin ya shaidawa kotun cewa yana dukan matar da yaran ne kawai idan suka aikata laifi, kuma yana yin hakan don gyara masu tarbiya. Alkalin ya ba shi shawara.
Mai shari’a Hakeem Oshodi na wata babbar kotu a Legas, ya gargadi jama’a da su daina barin layoyi a kotunsa domin ba sa aiki kuma. Ya yi gargadin yayin zaman kotu.
Kotun Kostamare
Samu kari