Bayan Ganawa da Tinubu, An Kara Zuga Gwamna Abba kan Rabuwa da Kwankwaso

Bayan Ganawa da Tinubu, An Kara Zuga Gwamna Abba kan Rabuwa da Kwankwaso

  • Batun sauya shekar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf zuwa APC na ci gaba da jan hankali bayan ganawarsa da Shugaba Bola Tinubu
  • Alhaji Liadi Tella ya shawarci Gwamma Abba ya shiga APC ko da kuwa ubangidansa kuma jagoran NNPP, Rabiu Kwankwaso bai yarda ba
  • Jigon APC ya ce sauya shekar gwamnan zai ba shi damar tsayawa da kafarsa, kuma ya samu taimakon gwamnatin tarayya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Wani jigo a APC, Alhaji Liadi Tella ya tsoma baki a siyasar Kano bayan ganawar da aka yi jiya tsakanin Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Abba Kabir Yusuf.

'Dan siyasar ya bukaci gwamnan Kano da ya dauki "mataki na jarumtaka da dabara" ta hanyar komawa APC, ko da kuwa ubangidansa na siyasa, Rabiu Musa Kwankwaso bai amince ba.

Kara karanta wannan

An gama magana: Shugaba Tinubu ya sharewa gwamnan Kano fagen shiga APC

Gwamnan Kano.
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf lokacin da yake jawabi a wurin taron Kwankwasiyya Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Facebook

An kara zuga Abba ya bar Kwankwaso

Yayin da yake zantawa da jaridar The Guardian, Liadi ya bayyana cewa tafiya tare da APC da Shugaba Tinubu zai ba wa Gwamna Abba damar samun karfin fada a ji fiye da ya ci gaba da zama karkashin inuwar Kwankwaso.

“Idan Gwamna Abba ya ci gaba da zama karkashin ikon Kwankwaso har zuwa 2027, babu makawa sai abu guda ya faru, ba zai samu tikitin takara ba a karkashin NNPP.
“Saboda haka komawa APC ba dabarar siyasa ba ce kawai, zai kuma tabbatar masa da cin gashin kansa, zai zama jagoran jam’iyya a Kano, ba tare da takura daga kowane ubangidan siyasa ba.”

Yadda rikici ya turnike Kwankwasiyya

Abba, wanda tsohon kwamishina ne a karkashin Kwankwaso, ya lashe zaben gwamnan Kano a 2023 da taimakon Kwankwasiyya da NNPP, wanda hakan ya kawo karshen mulkin APC na shekaru takwas a Kano.

Kara karanta wannan

Abubuwan da Abba Kabir ya tattauna da Tinubu ana maganar shigarsa APC

Tun bayan hawansa mulki, masu sharhi kan al’amuran siyasa sun lura da rikicin da ke tasowa tsakanin Abba da ubangidansa, musamman kan batun nade-nade, tsara manufofin gwamnati, da iko da jam’iyya, in ji rahoton The Nation.

Wadannan matsaloli sun kara rura wutar jita-jitar sauya shekar gwamnan Kano, musamman yayin da APC ke kara kaimi wajen ganin ta kwace Kano a zaben 2027.

Liadi Tella ya nanata cewa shiga APC zai ba gwamnan ikon gudanar da mulkin Kano tare da hadin gwiwar gwamnatin tarayya ba tare da tsangwama ba.

Jagoran NNPP na kasa.
Jagoran NNPP na kasa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso yana jawabi ga magoya bayansa Hoto: @SaifullahiHON
Source: Facebook

Tinubu da APC na bukatar Kwankwaso?

Game da tasiri karfin siyasar Kwankwaso kuwa, Liadi ya tabbatar da cewa tsohon gwamnan Kano ya fara rasa kima da farin jininsa a matakin kasa.

Ya ce:

“Ba na jin Shugaba Tinubu ko APC na bukatar Kwankwaso kafin su yi nasara a Kano a 2027, idan aka yi la’akari da yanayin siyasar jihar a halin yanzu.”

Tinubu ya sharewa Abba hanyar shiga APC

A wani labarin, kun ji cewa bayanai sun nuna cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya shirya sauya sheka daga NNPP zuwa APC bayan ganawarsa da Shugaba Tinubu.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta yi magana kan ganawar Bola Tinubu da gwamnan Kano

Majiyoyi da dama da ke da masaniya kan ganawar sun bayyana tattaunawar ta warware muhimman matsalolin da suka jawo jinkirin komawar Abba APC.

Majiyoyi sun ce shugaban kasa ya tabbatar wa Abba Gida-Gida da kansa cewa za a daraja shi a APC, musamman a Kano da kuma yankin Arewa maso Yamma.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262