Zaben Anambra: Dan Takarar ADC Ya Gano Lam'a a Zabe, ya Ce Bai Gamsu da Sakamako Ba

Zaben Anambra: Dan Takarar ADC Ya Gano Lam'a a Zabe, ya Ce Bai Gamsu da Sakamako Ba

  • Dan takarar gwamna a ADC a jihar Anambra y ace sam bai gamsu da zaben da aka gudanar ranar Asabar ba
  • Nwosu ya bayyana yadda aka yi cinikin kuri’u da kuma musayar kudi don tabbatar da zaben jam’iyyar APGA
  • A gefe guda, shugaba Tinubu ya bayyana murna da jin dadi yayin da Soludo ya sake nasara a zaben na Anambra

Jihar Anabmra - John Nwosu, dan takarar jam’iyyar ADC a zaben gwamnan da aka gudanar a ranar 8 ga Nuwamba a jihar Anambra, ya yi watsi da sakamakon zaben yana mai cewa “ba gaskiya ba ne kuma an tauye muradin jama’a gaba daya.”

A cewar sakon da ya fitar bayan kammala zaben, Nwosu ya ce an jirkita tsarin zaben ta hanyar sayen kuri’u da cin hanci a kusan dukkanin rumfunan zabe a fadin jihar.

Idan baku manta ba, an sanar da cewa, dan takarar jam’iyyar APGA), Charles Soludo ne ya lashe zaben da kuri’u 422,664, yayin da Nicholas Ukachukwu na APC ya samu kuri’u 99,445, sai kuma Nwosu wanda ya samu kuri’u 8,208 kacal.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yi magana kan zaben Anambra, ya aika sako ga Gwamna Soludo

Dan takarar gwamna a ki amincewa da sakamako
Lokacin da John Nwosu ke yin watsi da sakamakon zabe a Anambra | Hoto: @JohnCNwosu
Source: Twitter

Farfesa Edoba Omoregie, wanda shi ne Shugaban Jami’ar Benin kuma Jami’in tattara sakamakon zabe na INEC, shi ne ya bayyana sakamakon a ranar Lahadi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ban gamsu da sakamakon ba, Nwosu

Amma Nwosu ya dage cewa mutanen Anambra ba su samu ra’ayinsu ba, yana zargin cewa zaben ya zama kasuwanci maimakon dimokuradiyya, inda ake bai wa masu kada kuri’a kudi daga N3,000 zuwa N20,000.

A kalamansa:

“Wannan abin kunya ne ga kasa da kuma cin zarafin dimokuradiyyarmu. Nasara da aka saya da kudi, ba nasara ba ce, illa asara ga gaskiya da adalci.
“Gaskiyar nasara ba ta cikin sakamako, tana cikin tsarkin tsarin da aka bi. Zaben da ya cika da rashawa, magudi da cinikin kuri’a ba zai taba zama muradin jama’a ba.”

Akwai laifin hukumomi, inji Nwosu

Ya kuma soki hukumomi da sauran cibiyoyi da ya ce sun kasa kare amincin kuri’ar jama’a, yana mai cewa idanuwan duniya sun ga yadda adalci ya fadi kasa a zaben.

Kara karanta wannan

Zabe ya bar baya da kura, an bindige kansila yayin jefa kuri'a a Anambra

Ya gode wa jam’iyyarsa ADC, da kungiyar yakin neman zabensa, saboda tsayawa da gaskiya da kwarin gwiwa duk da tsoratarwa da tayin kudi.

Sai dai, ba karon farko kenan ba da ‘yan siyasa ke kalubalantar juna bayan zabe ba, hakan yakan faru a kusan karshen kowanne zabe.

Tinubu ya taya Soludo murna

A gefe guda, Shugaban kasa Bola Tinubu ya taya Gwamna Charles Soludo murnar sake lashe zaben gwamnan Anambra karo na biyu, yana mai cewa hakan shaida ce ta jagoranci nagari da amincewar jama’a gare shi.

A cikin wata sanarwa daga fadar shugaban kasa a Abuja, Tinubu ya ce nasarar Soludo ta kafa tarihi a siyasar Anambra, inda ya zama gwamna na uku da ya sake lashe wa’adi na biyu.

Ya kuma yaba da mutanen Anambra, jami’an tsaro da hukumar INEC saboda zabe cikin aminci kuma ya gudana cikin kwanciyar hankali.

A cewar Tinubu:

“Sake zaben Soludo shaida ce ta hangen nesa da jagoranci nagari. Ya nuna cewa ilimi da gaskiya suna iya canza mulki idan aka yi amfani da su cikin kwarewa da gaskiya.”

Kara karanta wannan

Bidiyo: An ga 'yan sanda suna harba bindiga bayan Soludo ya lashe zaben Anambra

Irin ayyukan ci gaba da aka yi a Anambra

Ya kara da cewa, lokacin da ya kai ziyara jihar Anambra a watan Mayu, ya ga ayyukan ci gaba da Soludo ke aiwatarwa ci gaba.

Shugaban kasar ya bukaci Soludo da ya yi hakuri da masu adawa, ya kuma nemi hadin kai don ci gaban jihar.

Tinubu ya kuma yaba da sabon Shugaban INEC, Joash Amupitan, saboda gudanar da zabe mai inganci da gaskiya, yana mai cewa ya kamata hukumar ta ci gaba da kara kyautata tsarin ta domin karfafa dimokuradiyyar Najeriya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and leads the Hausa Desk at Legit.ng. He is AfricaCheck's ambassador and HumAngle Technology and Civic Impact Fellow. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. His commitment to excellence has earned him recognition, including the Legit Fearless Team Player of the Year 2023 and 2024 Distinguished Editorial Leadership Award. Email: salisu.ibrahim@corp.legit.ng