INEC Ta Ɗage Tattara Sakamakon Zaben Gwamnan Anambra, Ta Sanya Sabon lokaci

INEC Ta Ɗage Tattara Sakamakon Zaben Gwamnan Anambra, Ta Sanya Sabon lokaci

  • INEC ta dakatar da tattara sakamakon zaben gwamnan Anambra yayin da ake jiran sauran kananan hukumomi biyu
  • Farfesa Edogah Omoregie, jami’in tattara sakamakon jihar, ya ce an kammala tattara sakamakon kananan hukumomi 19
  • Gwamna Charles Soludo na APGA na kan gaba da kuri’u 389,789, inda yake kan hanyar lashe zabe a karo na biyu

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Anambra - Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta dakatar da tattara sakamakon zaben gwamnan Anambra da aka gudanar a ranar Asabar.

An dakatar da tattara sakamakon ne bayan kammala bayyana sakamakon zaben kananan hukumomi 19 daga cikin 21 da ke jihar.

INEC ta dage tattara sakamakon zaben gwamnan jihar Anambra
Hoton cibiyar tattara sakamakon zaben gwamnan Anambra da ke a hedikwatar INEC, a birnin Awka. Hoto: @SituationRoomNg
Source: Twitter

INEC ta dakatar da tattara sakamakon zabe

Jami’in tattara sakamakon jiha, Farfesa Edogah Omoregie na jami’ar Benin, ne ya sanar da hakan da safiyar Lahadi a cibiyar hukumar da ke Awka, babban birnin jihar, in ji rahoton Punch.

Kara karanta wannan

Sakamakon zaben Anambra: Yadda APGA ta samu kuri'u 422664 a kananan hukumomi 21

Ya bayyana cewa tattara sakamakon zai ci gaba da karfe 6:00 na safe, yayin da ake jiran sakamakon kananan hukumomi biyu.

An rahoto cewa jami'an tattara sakamakon zaben kananan hukumomin biyu ba su kai ga isowa cibiyar ba saboda jinkiri wajen isar da kayan aikin zabe da kuma nisan wuraren.

“Mun kammala tattara sakamakon kananan hukumomi 19, saura biyu da muke jiran sakamakonsu. Don haka za mu dakata, sai zuwa karfe 6:00 na safiya za mu ci gaba."

- In ji Farfesa Omoregie.

Anambra: Soludo ya samu kuri'u masu yawa

Har zuwa lokacin da aka dakatar da tattara sakamakon, dan takarar jam’iyyar APGA, Gwamna Charles Chukwuma Soludo, shi ke kan gaba da babban rinjaye a zaben.

Jaridar The Cable ta rahoto cewa, sakamakon kananan hukumomi 19 da aka bayyana ya nuna cewa:

  • APGA (Soludo) na da kuri'u 389,789.
  • APC (Nicholas Ukachukwu) na da kuri'u 91,592.
  • LP (George Moghalu) na da kuri'u 10,366.
  • PDP (Jude Ezenwafor) na da kuri'u 1,230.

Kara karanta wannan

Anambra 2025: Soludo ya lallasa APC, LP, ya ci zabe a dukkan kananan hukumomi 21

Wannan sakamakon ya nuna cewa Soludo yana da rinjaye sosai, kuma yana da dama mai karfi ta samun nasara idan sakamakon saura kananan hukumomin biyu bai zo da babban sauyi ba.

An ruwaito cewa Gwamna Charles Soludo na jam'iyyar APC ne ke kan gaba da tazarar kuri'u masu yawa.
Gwamna Charles Soludo na jihar Anambra a lokaci da aka karrama shi. Hoto: @CCSoludo
Source: Facebook

INEC ta dora 95% na sakamakon zaben Anambra

INEC ta bayyana cewa ana gudanar da tattara dukkanin sakamakon zaben ne a cibiyarta da ke Awka, inda sakamakon daga rumfunan zabe ke isa daga sassan jihar.

Hukumar ta kara tabbatar da cewa an riga an loda kashi 95 cikin 100 na sakamakon zaben a shafinta na IReV, wanda ke tabbatar da gaskiya da ingancin tsarin.

INEC ta ce na'urar BVAS da aka yi amfani da ita ta taimaka wajen rage kura-kurai da karfafa sahihancin zabe, tare da ba da tabbacin cewa sakamakon karshe zai kasance mai gaskiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com