"40% Ake ba Shi," El Rufai Ya Zargi Uba Sani da Yin Kashe Mu Raba da Yan Kwangila

"40% Ake ba Shi," El Rufai Ya Zargi Uba Sani da Yin Kashe Mu Raba da Yan Kwangila

  • Nasir El-Rufai ya zargi Gwamna Uba Sani da karɓar kaso 40% daga ƴan kwangila kafin ya amince ya ba su aiki a jihar Kaduna
  • Tsohon gwamnan ya bayyana cewa ba haka gwamnatinsa ta yi ba, hasali ma bai cika haɗuwa da ƴan kwangilar da ake ba aiki ba
  • El-Rufai ya ce ya kaucewa duk wasu harkokin cin hanci da rashawa ne ba don tsoron EFCC ko ICPC ba sai don tsoron Allah SWT

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya sake jaddada cewa bai karɓi ko kwabo daga ƴan kwangila ba har ya sauka daga mulki a 2023.

El-Rufai ya ce a shirye yake kuma ba ya jin tsoron kowa domin bai taɓa ɗaukar ko kwandala daga asusun gwamnatin Kaduna ba a tsawon shekaru takwas da ya yi.

Kara karanta wannan

'Yadda Ribadu ya hada kai da ICPC domin kai ni kurkuku kafin zaben 2027' - El-Rufai

Uba Sani da El-Rufai.
Malam Nasir El-Rufai ya tona yadda ake kashe nu raba da gwamna kafin ba da kwangila a Kaduna Hoto: Nasir El-Rufai, Uba Sani
Asali: Facebook

Malam Nasir ya yi wannan furuci ne a wata hira da aka yi da shi a Freedom Radio Kaduna wadda Legit Hausa ta bibiya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

El-Rufai ya zargi Uba Sani da karɓar 40%

Tsohon gwamnan ya kuma zargi gwamna mai ci, Sanata Uba Sani da yin kashe mu raba da ƴan kwangila kafin ya ba su aiki a Kaduna.

A cewarsa, a yanzu duk wanda za a ba kwangila sai ya ga gwamna kuma ya cire masa kaso 40% gabanin ya samu wannan aiki.

Nasir El-Rufai ya yi ikirarin cewa a gwamnatin yanzu, Uba Sani na kwasar takardun kwangila ya nufi Abuja, ya karɓi kason shi sannan ya miƙawa ƴan kwangila.

Yada ake kashe mu raba da Uba Sani

"A irin gwamnatinsu ta yanzu, mutum bai iya samun kwangila sai ya ga gwamna, sai ya ba gwamna kaso 40%, abin da Uba yake yi kenan, da takardun kwangila yake zuwa Abuja, ya na bayarwa ana ba shi kudi."

Kara karanta wannan

'Za ku ga karshen su,' El Rufa'i ya yi Allah ya isa ga 'yan majalisar Kaduna

"Duk mun san abin da suke yi, kowa a garin nan ya na magana kan wannan, sun ɗauka haka muka yi a gwamnatinmu, ba haka muka yi ba, ba haka muka yi ba wallahi.
"Kuma ba wai mun ƙi yin haka ba ne don tsoron EFCC ko ICPC, a'a ko kaɗan ba haka ba ne, mun guje wa haka ne don tsoron Allah, me za su iya yi, an kama Bashir Saidu an kai shi kurkuku, ya mutu ne?"

- In ji El-Rufai.

Malam Nasir El-Rufai.
Tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya zargi Uba Sani da karɓar kaso 40% daga hannun ƴan kwangila Hoto: Nasir El-Rufai
Asali: Facebook

"Mu na jin tsoron Allah" - El-Rufai

Tsohon gwamnan ya ce gwamnatinsa ta kaucewa harkokin rashin gaskiya ne ba don tsoron EFCC ba sai don tsoron Allah Maɗaukakin Sarki.

Ya ce babu abin da wani ɗan adam zai iya maka matukar Allah bai kaddara faruwat hakan a rayuwarka ba.

El-Rufai ya ce da dama daga cikin ƴan kwangilar da aka ba aiki a gwamnatinsa ba su taɓa ganinsa ba, domin a cewarsa, babu wata hulɗa da za ta haɗa shi da su.

Kara karanta wannan

El-Rufa'i: "Kwangilar Tinubu Uba Sani ce ya karbo domin karya ni a siyasa"

'Badakalar kudin kananan hukumomi'

A wani labarin, kun ji cewa Nasir El-Rufai ya zargi Gwamna Uba Sani da karkatar da kuɗin kananan hukumomi ta hanyar sayen kadarori a ƙasashen waje.

Malam El-Rufai ya bayyana kasashen uku da yake zargin Uba Sani na sayen kadarori da kudin kananan hukumomin Kaduna da aka turo daga tarayya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel