Abin da Shugaban BoT Ya Faɗa a Wurin Taron PDP bayan an Mari Babban Jigo a Abuja

Abin da Shugaban BoT Ya Faɗa a Wurin Taron PDP bayan an Mari Babban Jigo a Abuja

  • Shugaban BoT na PDP ta ƙasa, Sanata Adolphus Wabara ya ce ya zama dole a shirya taron kwamitin zartarwa watau NEC nan kusa
  • Wabara ya bayyana haka ne a taron BoT karo na 76 wanda rigima ta kaure kan rikicin kujerar sakataren PDP na ƙasa a Abuja ranar Laraba
  • Ya kuma soki gwamnatin APC yana mai cewa har yanzun ƴan Najeriya na kallon PDP a matsayin jam'iyyar da za ta iya ceton ƙasarsu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban Majalisar Amintattu (BoT) na jam’iyyar PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya jaddada cewa dole ne a gudanar da taron kwamitin zartarwa (NEC) da aka shirya yi a watan Fabrairu.

Sanata Wabara ya ce duk da rikicin shugabanci da ke ci gaba da addabar PDP, ya zama dole a shirya taron NEC nan kusa don warware wasu matsalolin.

Kara karanta wannan

Gwamoni sun kira taron gaggawa bayan an ba hamata iska a taron PDP

Taron BoT.
Shugaban BoT ya nanata bukatar gudanar da taron NEC kamar yadda aka tsara a watan Fabrairu, 2025 Hoto: @OfficialPDPNig
Asali: Twitter

Wabara ya yi wannan bayani ne a taron BoT karo na 79 da aka yi a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja a ranar Laraba, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda rigima ta ɓarke a taron BoT

Taron BoT na wannan karon ya zo da tashin-tashina, inda masu rigima kan kujerar sakatare, Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye suka yi arangama.

Rahoto ya nuna cewa faɗa ya kaure a wurin taron har sai ta kai ga marin Ude-Okoye tare da fitar da shi daga ɗakin taron da ƙarfin tsiya.

Rikicin ya yi ƙamari a jiya Laraba har dai da jami'an tsaro suka shiga tsakani, sannan komai ya lafa a hedkwatar PDP ta ƙasa.

Abin da shugaban BoT ya faɗa a taron

Da yake jawabi a wurin taron, shugaban BoT ya bukaci ƴan PDP a kowane mataki su haɗa kansu kuma ya ja hankalinsu da su fifita ci gaban jam’iyya fiye da bukatun kansu.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta samo rancen sama da N1bn don tsame Najeriya daga duhu

"Wannan taro ya zo ne a daidai lokacin da hadin kai, manufa, da ƙimar jam’iyyarmu ke fuskantar kalubale. Abin takaici ne har yanzu ba a warware rikicin shugabanci a kwamitin gudanarwa (NWC) ba.
"Rashin shawo kan wadannan matsaloli yana rage wa jam’iyyarmu mutunci," in ji Wabara.

Ya kamata PDP ta shirya taron NEC

Ya kara da cewa yana da matukar muhimmanci a gudanar da taron NEC kamar yadda aka tsara a wata mai kamawa.

"NEC ita ce mai alhakin yanke shawara a jam’iyyarmu, dole ne a gudanar da taron ba tare da bata lokaci ba domin mu tabbatar da an rungumi hadin kai, da’a, da manufofin da suka hada mu wuri guda."

Adolphus Wabara ya kuma caccaki jam’iyyar APC, yana mai cewa PDP ce kadai za ta iya ceto Najeriya, kamar yadda Punch ta ruwaito.

"Kasar mu tana wahala a karkashin mulkin APC. ‘Yan Najeriya na kallonmu a matsayin haske da fatansu na gari, dole ne mu cika wannan buri," in ji shi.

Kara karanta wannan

Manyan ƙusoshi 2 sun yi arangama a wurin taron majalisar amintattun PDP a Abuja

Damagum ya zargi wasu shugabanni a taron BoT

A wani labarin kun ji cewa muƙaddashin shugaban PDP na ƙasa ya zargi wasu shugabanni da hannu a rura wutar rikicin da ke faruwa a NWC.

Umar Damagum ya ce lokaci ya yi da za a haɗa kai wuri guda domin farfaɗo da jam'iyyar PDP wacce ƴan Naheriya ke da sa rai a kanta.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

iiq_pixel