Gwamnoni da Jiga Jigai Sun Gano Abin da Zai Hana PDP Ƙwace Mulki daga Tinubu a 2027

Gwamnoni da Jiga Jigai Sun Gano Abin da Zai Hana PDP Ƙwace Mulki daga Tinubu a 2027

  • Gwamnoni da shugabannin PDP na kasa sun nuna damuwa kan rikicin cikin gida da ya ƙi karewa a babbar jam'iyyar adawar
  • Sun ce matukar ba a binne duk wani saɓani ba, rikicin ka iya kawo cikas a kokarin PDP na komawa kan madafun iko a 2027
  • Wannan na kunshe ne a sanarwa da gwamna Bala Mohammed, shugaban kungiyar gwamnonin PDP ya fitar bayan taronsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Gwammoni da masu ruwa da tsakin PDP sun yi gargaɗin cewa rigimar da ke faruwa a jam'iyyar ka iya wargaza shirinsu na karɓe mulki a zaɓen 2027.

Sun hango wannan matsala ne a taron da ya gudana karƙashin kungiyar gwamnonin PDP a Abuja ranar Talata da daddare.

Kara karanta wannan

Bayan Tinubu ya kori ministoci 5, ɗan takarar gwamna ya dawo jam'iyyar APC

GwamanonIn PDP.
Gwamnoni da masu ruwa da tsakin sun nuna damuwa kan rikicin cikin gida a PDP Hoto: @SenBalaMohammed
Asali: Facebook

Kamar yadda Leadership ta kawo, a wannan taron jam'iyyar PDP ta sake ɗage taron majalisar zartaswa watau NEC karo na biyu zuwa ranar 28 ga Nuwamba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kusoshin PDP sun halarci taro da gwamnoni

Masu ruwa da tsakin PDP da suka halarci taron ranar Talata sun haɗa da kungiyar gwamnonin jam'iyyar da kwamitin amintattu watau BoT.

Sauran sun haɗa da kwamitin gudanarwa NWC, ƴan majalisar tarayya na jam'iyyar da ƙungiyar tsofaffin gwamnoni.

Sanarwa da aka fitar bayan taron ɗauke da sa hannun gwamnan Bauchi kuma shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Bala Muhammed, ta nuna damuwa kan rikicin cikin gida.

Jam'iyyar PDP ta ɗauki matakin magance rikici

Sanarwar ta ce:

"A koƙarin haɗa kan ƴaƴan PDP da turmushe masu zagon ƙasa, jam'iyya ta buƙaci mambobinta su dunƙule wuri ɗaya, ka da su aminta da masu yunkurin ruguza jam'iyya.

Kara karanta wannan

Rikicin PDP: Daga karshe an fadi yankin da zai samar da shugaban jam'iyyar na kasa

"Taron ya kuma buƙaci ƴaƴan jam'iyyar su yi watsi da kalaman da ka iya raba kawunansu wanda za su iya gurgunta ƙoƙarin da ake na dawo da PDP kan turba da shirin karɓe mulki a 2027."

This Day ta ce PDP na fama da rikicin cikin gida musamman tsakanin tsagin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da ministan Abuja, Nyesom Wike.

Jigon PDP ya yi magana kan shugabancin jam'iyya

A wani rahoton kuma kun ji cewa ana ci gaba da shirye-shiryen wanda zai karɓi ragamar shugabancin jam'iyyar PDP na ƙasa daga hannun Umar Iliya Damagum.

Tsohon sakataren yaɗa labaran PDP na ƙasa ya bayyana cewa yankin Arewa ta Tsakiya ne zai samar da wanda zai canji Damagum.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262