Minista Ya Shiga Matsala, An Buƙaci Shugaba Tinubu Ya Kore Shi daga Aiki Nan Take

Minista Ya Shiga Matsala, An Buƙaci Shugaba Tinubu Ya Kore Shi daga Aiki Nan Take

  • Matasa sun buƙaci a kori ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu da shugaban kamfanin rarraba wuta na ƙasa TCN
  • Ƙungiyar matasan NYTGG ta ce akwai sakaci a yawan lalacewar babban layin lantarki wanda ya samu matsala sau uku a mako guda
  • A cewar kungiyar, rashin wuta ya jefa ƴan Najeeiya cikin duhu, ƴan kasuwar da ke amfani da lantarki sun tafka asara mai yawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Ga dukkan alamu rashin hasken wuta ya fara damun ƴan Najeriya yayin da wasu matasa suka roƙi a kori ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu.

Wata ƙungiyar matasan Najeriya (NYTGG) ta buƙaci a kori ministan wutar lantarki tare da shugaban kamfanin raba wuta TCN, Sule Ahmed Abdulaziz.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun hallaka matafiya, sun yi awon gaba da manoma a Neja

Adebayo Adelabu.
Matasa sun buƙaci Bola Tinubu ya kori ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu Hoto: Adebayo Adelabu
Asali: Twitter

Meyasa aka nemi korar minista da shugaban TCN?

Matasan sun nemi a sallami waɗannan mutane biyu daga aiki ne saboda yawan katsewar babbar layin wuta na ƙasa a ƴan kwanakin nan, Leadership ta kawo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban ƙungiyar matasa ta NYTGG, Abdullahi Sani ne ya faɗi hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Kaduna.

Ya ce abubuwan da ke faruwa a ɓangaren samar da wutar lantarki da rarraba ta abin damuwa ne kuma kullum babu gyara sai ƙara taɓarɓarewa.

Abdullahi ya koka cewa rashin wuta ya jefa mutane da yawa a duhu, ƴan kasuwa sun yi asara sannan tattalin arzikin ƙasa ya samu koma baya.

A cewarsa, daga hawan Tinubu kan madafun iko zuwa yanzu, wutar lantarki ta lalace sau da dama wanda ya haddasa rashin hasken wuta a mafi yawan sassan ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Sankara: Kotu ta ba 'yan sanda umarni kan kwamishinan Jigawa da aka dakatar

Rashin wuta: Matasa sun nemi a ɗauki mataki

A rahoton Daily Post, shugaban NYTGG ya ce:

"Duba da wannan muna kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya sunan Adebayo Adelabu a cikin wadanda za a sallama idan ya tashi garambawul a majalisar zartaswa."
"Ya zama dole a ɗauki tsattsauran mataki kan yawan lalacewar babban layin wutar lantarki, bai kamata a bar lamarin sakaka ba,"

TCN ya yi bayanin lalacewar wutar lantarki

A wani labarin kuma kamfanin TCN ya bayar da rahoton lalacewar wutar lantarki a Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya.

Manajan hulda da jama’a na TCN, Ndidi Mbah ya bayyana cewa wasu layukan wuta da ke kan tashar Ugwaji-Apir ne suka samu matsala.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262