Bayan Shan Kaye a Zaben Edo, Dan Takarar Gwamna a LP Ya Dauki Sabon Mataki

Bayan Shan Kaye a Zaben Edo, Dan Takarar Gwamna a LP Ya Dauki Sabon Mataki

  • Dan takarar gwamnan jihar Edo karkashin jam'iyyar Labour (LP), Olumide Akpata ya ce ba zai kalubalanci sakamakon zaben a kotu ba
  • Olumide Akpata ya ce ya dauki wannan matakin ne bayan tattaunawa mai zurfi da tawagar lauyoyinsa da kuma masu ruwa da tsaki
  • A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Asabar, Akpata ya yi cikakken bayani kan matakinsa da yadda aka yi zaben jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Edo - Olumide Akpata, dan takarar jam’iyyar Labour (LP) a zaben gwamnan jihar Edo, ya sake daukar sabon mataki bayan ya sha kaye a zaben da ya gabata.

Akpata ya yi ikirarin cewa an tafka kura-kurai a zaben na Edo kamar sayen kuri’u da kuma saba dokar tattara sakamakon zaben wanda ba a taba ganin irinsa ba.

Kara karanta wannan

Likitoci, lauyoyi sun nemi Tinubu ya warware matakin NNPCL da fetur ya kai N1030

Olumide Akpata ya yi magana kan zuwa kotu domin kalubalantar zaben gwamnan Edo
Dan takarar Labour ya ce ba zai kalubalanci zaben gwamnan jihar Edo a kotu ba. Hoto: @OlumideAkpata
Asali: Facebook

Duk da wadannan kalubale, jaridar The Cable ta rahoto cewa Olumide Akpata ya ce ba zai kalubalanci sakamakon zaben jihar a kotu ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dalilin Akpata na kin zuwa kotu

A wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Asabar, Akpata ya ce matakin da ya dauka na kin kalubalantar sakamakon zaben ya biyo bayan lissafin siyasa.

"Yayin da aka rufe kofar shigar da kara a kotun sauraron kararrakin zaben gwamna, mun tsaya a wani muhimmin mataki a jihar Edo da kuma dimokradiyyar Najeriya.
“Bayan tattaunawa mai zurfi da tawaga ta lauyoyi da masu ruwa da tsaki, na yanke shawarar kin kalubalantar sakamakon zaben da aka gudanar a gaban kotun."

"An tafka kura kurai" - Akpata

Akpata ya ce kura kuran da aka tafka a zaben gwamnan jihar Edo ya zarce duk wanda aka taba gani a jihar a baya, inji rahoton Arise News.

Kara karanta wannan

Hadimin Atiku ya gama bayanin yadda za a sasanta rikicin PDP, lissafi ya watse a ranar

Babban lauyan ya ce rashin bin ka’ida “alama ce ta gurbacewar tsarin siyasa” da ke addabar tsarin zaben kasar nan.

Ya ce:

"Wannan ba cin zarafin fasaha ne kadai ba, har ma da keta haddi na zamantakewa tsakanin gwamnati da wadanda ake mulka"

Sakamakon zaben gwamnan Edo

Legit Hausa ta rahoto cewa hukumar INEC ta ayyana Monday Okpebholo, dan takarar jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 21 ga watan Satumba.

Okpebholo ya samu kuri’u 291,667 inda ya doke Asue Ighodalo na PDP wanda ya samu kuri’u 247,274 yayin da Olumide Akpata ya zo na uku a zaben da kuri’u 22,763.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.